Sunday 1 October 2017

Babu Babban Munafiki kamar Obasanjo-Ola Ishola-Williams

Tura Wannan Zuwa

Ola Ishola-Williams ya ce Obasanjo munafuki
ne
Manjo Janar Ola Ishola-Williams mai ritaya ya
caccaki tsohon shugaban Najeriya, Cif Olusegun
Obasanjo a kan shawarci ga shugaba
Muhammadu Buhari don tattaunawa da Nnamdi
Kanu shugaban kungiyar ‘yan asalin yankin
Biyafara, IPOB.

Kamar yadda NAIJ.com ke da labari, Williams ya
ce Obasanjo bai kamata ya kasance mai magana
game da tattaunawa ba, yana tuna cewa a
matsayin shugaban kasa, ya umarci kai hari a
kan al'ummomi ba tare da yin shawarwari ba.
"Tattaunawa ya kamata ya zama mafi kyawun zaɓi a
warware rikicin. Amma na fi son shugaba Buhari ya
tattauna tare da shugabannin ‘yan kabilar Igbo
wato Ohanaeze da gwamnatocin kudu maso gabas
da kuma sauran shugabannin yankin wadanda ke
kokari wajen magance matsalar", inji shi.

Shawarar Obasanjo ba daidai ba ne. Yaya Buhari
zai kira Kanu don ya tattauna da shi? Idan shugaba
Buhari ya yi hakan, zai iya kawo tikas ga kokarin da
Ohaneze da gwamnonin yankin ke yi don neman
mafita ga rikicin".

"Ya kamata Obasanjo ya kama bakinsa, idan bai
san abin da zai ce ko ba da shawara ba. Da
girmamawa, Obasanjo munafuki ne”.

"Lokacin da yake shugaban kasa tsakanin 1999 da
2007, ya gayyaci kowa don tattaunawa kafin ya tura
dakaru don kai hari a Odi a jihar Bayelsa da Zaki
Biam a jihar Binuwai?”.

"Ba shugaba Buhari shawara ya sadu da Kanu,
Obasanjo yana halatta ayyukan Nnamdi Kanu wanda
ba daidai ba ne?, in shi.

"

.
Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa kamar haka  dadinkowa24.blogspot.com mungode
.
Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa nayau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com
.
Idan kana/kina da Labarin daku keson asanarwa da Duniya, ko Tambaya,Shawarwari,Hausa Novels, Nishadantarwa,Ilimantarwa,Ko Neman Sani akan ranakun dazamu cigaba dakawo muku Posting na Hausa Novels da Sauran su, zaku iya tuntubar ma'aikatan mu kuturo da Sunan Ku tareda Addreshin Ku tawannan Email din Officialdadinkowa24@gmail.com kyautane zamuyi muku komai don cigaban Al'ummar Hausa bama bukatar kudinka sai dai idan kaikayi niyyar Turowa don siyan Data Saboda acigaba dayin Posting a Kodayaushe batareda dakatawa ba, Website din Mu bashi da Alaka ta kusa ko tanesa da Wani/Wata Dan Siyasa/'Yar Siyasa afadin Duniya Burin mu shine musamu amincewar Al'umma aika da Gudunmawarka,Labari,Shawara da sauran su a Addreshin mu na email ✉💌📩 officialdadinkowa24@gmail.com
.
Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com
.
Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri
.
ALLAH yabar Zumunci Amin🙏
.
.
Source By ©Abdul'azeez Abdul

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: