Thursday 15 March 2018

Kalli Yadda Majalisar Dinkin Duniya ta karrama Rahama Sadau- Bude Ku Kalli Hotunan

Tura Wannan Zuwa

An karrama jarumar fina-finan Hausa ta Kannywood ta arewacin Najeriya Rahama Sadau, a wurin bikin ba da lambar yabo ta jaruman fina-finai mata Women Illuminated Film Festival, wanda aka yi a gefen taron Majalisar Dinkin Duniya.

Jarumar ta wallafa hotunan bikin bayar da kyautukan da aka yi a birnin New York a ranar Litinin a shafinta na Instagram, tana mai nuna matukar jin dadinta.

Rahama ta rubuta cewa: "Wannan girmamawa ce babba a gare ni, na ji dadi matuka, kuma ina alfaharin kasancewa a wannan daren tare da hazikan mata da dama."

Ta kara da cewa: "Akwai wadansu lokuta a rayuwa da ya kamata mutum ya tsaya ya tambayi kansa, yaya aka yi ma na kawo nan? Babu ko tantama wannan na cikin irin wadannan lokutan wadanda har abada ba zan taba mantawa da su ba."

Abokan aikin Rahama da dama sun taya ta murna a shafukan sada zumunta kan wannan lambar yabo da ta samu.

Jarumi Ali Nuhu ya rubuta a shafinsa na Instagram cewa: "Ina taya ki murna 'yar uwata."

Ana yin wannan bikin na ba da lambar yabo ta jaruman fina-finai mata ne tare da hadin gwiwa da Majalisar Dinkin Duniya don nuna martaba mata masu yin fim.

Rahama Sadau dai a baya an sha samun ce-ce-ku-ce a kanta a masana'antar Kannywood, inda har a bara aka dakatar da ita sakamakon fitowar da ta yi a wani bidiyon waka tana "rungumar" wani mawaki.



Sai dai a watan Oktobar da ya gabata ne jarumar ta fito fili ta nemi gafarar duk wani mutum da bai ji dadi ba sakamakon abun da tayi.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku
Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu


Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Muryarhausa24.com don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum

An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com
Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Muryarhausa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki
daya Amin Summa Amin.

Source by ©Bbc Hausa
TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user