Saturday 30 September 2017

Karanta Kaji: Na shigo Kannywood da Izinin Iyayena – Maryam Yahaya

Tura Wannan Zuwa Ga
Tauraruwar matashiyar jaruma Maryam Yahaya, mai shekara 20, ta fara haskawa ne a cikin fim dinta na farko wato Mansoor.
A wata hira da Yusuf Ibrahim Yakasai, ta shaida masa ta taka rawar babbar jaruma a fim din duk da cewa shi ne fitowarta ta farko a fina-finan Kannywood, saboda ta kudurci aniyar taka rawar da masu shirya fim din suka umarce ta duk da kasancewarta sabuwar fitowa.

Ta kara cewa ainahi ba ita ce wadda za ta fito a matsayin jarumar fim din ba tun da fari, ta samu zama tauraruwar ne saboda rashin zuwan ainahin jarumar a kan lokaci, kuma daman tana cikin fim din sai dai fitowa biyu kadai aka shirya za ta yi.

Ta ce ”Ali Nuhu ne ya sanya aka zabo mu biyu a cikin wadanda za su yi fitowa ta musamman, ya ba mu rubutaccen labarin fim din muka karanta Allah cikin ikonsa sai na kasance wadda ta yi daidai abin da ya bukata, ka ji yadda akai na zama jarumar fim din Mansoor,” in ji jaruma Maryam.

Maryam ta kara da cewa: ”Da fari na dan ji tsoro, don ita dayar da aka ba mu labarin muka karanta tare ta ce kawai na je ina ta dari-dari. Ina farawa sai na ga an fara tafi da ihu kawai sai sarki Ali ya ce aje a fara aiki.”

Da aka tambaye ta ko yaya ta ji da aka ce ita ce, za ta zama tauraruwar fim din?
Sai ta kada baki ta ce ”Na ji wani dadi da ba zan iya fasalta yadda na ji ba, amma kam ina cikin tsananin farin ciki a wannan lokacin.” in ji Maryam.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode


Source By ©Bbc Hausa
TURA WANNAN ZUWA GA

Mawallafi: verified_user