Tuesday 10 October 2017

Shin ko Kasan Kasashen Afrika da ke hanyar tsallakewa zuwa Rasha???

Tura Wannan Zuwa

Bayan Nigeria da Masar sun samu nasarar shiga sahun kasashen da za su buga gasar cin kofin duniya da za a yi a Rasha a badi.

Yanzu Tunisia da Senegal da Morocco ke kan layi na fatar cike gibin gurbin na Afrika.

Kasashe 5 za su wakilci Afrika a gasar cin kofin duniya a Rasha
Tunisia na fuskantar barazana domin Jamhuriyyar Dimokuradiyar Congo na iya tsallakewa a rukuninsu na A.

Cote d’Ivoire na iya hanawa Morocco tsallakewa a rukuninsu na C.

Maki daya Morocco ta ba Cote d’Ivoire, kuma sai wasan karshe za a tantance tsakaninsu.

Tunisia dai na neman maki guda ne kacal a karawar da za ta yi da Libya.

Idan har Tunisia ta sha kasha, kuma DRC ta doke Guinea to zai kasance mai yawan kwallaye ne tsakaninsu zai tafi Rasha.

Rukunin da babu tabbas shi ne na D, domin Senegal da Burkina Faso da Cape Verde da Afrika ta Kudu dukkaninsu na da hasken zuwa Rasha.

Amma Senegal ta fi fatan samun nasara domin tana neman maki 2 a karawar karshe da za ta yi da Afrika ta kudu.

Burkina faso ce ta biyu da maki 6, haka ma Cape Verde tana da maki 6 a matsayi na uku, Afrika ta kudu ce ta karshe a rukunin.

A ranakun 6 da 14 ga Nuwamba ne kasashen za su fafata domin tantance sauran wadanda za su wakilci Afrika bayan Najeriya da Masar.

.
Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa kamar haka  dadinkowa24.blogspot.com
.
Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don ganin sabbin posting din Mu se ku duba saman website din akwai "Home" sai ku shiga, mungode
.
Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa nayau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com
.
Idan kana/kina da Labarin daku keson asanarwa da Duniya, ko Tambaya,Shawarwari,Hausa Novels, Nishadantarwa,Ilimantarwa,Ko Neman Sani akan ranakun dazamu cigaba dakawo muku Posting na Hausa Novels da Sauran su, zaku iya tuntubar ma'aikatan mu kuturo da Sunan Ku tareda Addreshin Ku tawannan Email din Officialdadinkowa24@gmail.com kyautane zamuyi muku komai don cigaban Al'ummar Hausa bama bukatar kudinka sai dai idan kaikayi niyyar Turowa don siyan Data Saboda acigaba dayin Posting a Kodayaushe batareda dakatawa ba, Website din Mu bashi da Alaka ta kusa ko tanesa da Wani/Wata Dan Siyasa/'Yar Siyasa afadin Duniya Burin mu shine musamu amincewar Al'umma aika da Gudunmawarka,Labari,Shawara da sauran su a Addreshin mu na email ✉💌📩 officialdadinkowa24@gmail.com
.
Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com
.
Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri
.
ALLAH yabar Zumunci Amin🙏
.
.
Source By ©Awwal Ahmad Janyau

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: