Wednesday 29 November 2017

FINA-FINAN HAUSA; GYARA KO BARNA???

Tura Wannan Zuwa

A wajajen shekarar 2013 zuwa 14, na yi wani
rubutu da ya janyo cece-kuce a da'irar fina-finan
Hausa, wanda karshe wasu ke kallon kiyayya ce
tsantsa ga masu sana'ar har ta sanya muke
bayyana wadannan maganganun. Bayan wannan,
na sha hakaito yadda wasu daidaikun mmalaman
jami'o'in Kasar nan suka fuskanci rashin kunya
daga wasu fitsararrun 'yan wasan, musamman
ganin yadda su malaman masana ne a game da
harshe da al'adun Hauwpsawa, wanda hakan ya
sa suke bayyana munanan hadarin fina-finan a
al'adance, kuma suka rinka kira a kan dole a zo a
yi gyara, amma karshe aka rinka yi musu rashin
kunya da fitsara ba tare da an duba matakinsu a
karatu ko matsayinsu a cikin al'umma ba.

A shekarar da ta gabata, na kai ziyarar ofishin
wani tsohon furodusa, marubuci, dan wasa kuma
darakta; bayan wata fira da aka yi da shi game
da yadda fina-finan Hausa na yanzu suka bar
tafarkin Hausawa da al'adunsu. Mun kara
tattauna makamanciyar abin da ya fada, sannan
ya nuna inda sababin kuskiuren ya faru.

Idan muka dawo kan batunmu, zai bayyana
karara a gabanmu yadda fina-finan Hausa a yau
suka mamaye gidaddajinmu da shagunanmu da
wayoyinmu.

Hakan sai ya sanya da dama cikin
mutane ke ganin wata hanya ce ta samun
sana'o'i halattacciya a bangarori daban-daban na
mutane.

Da zarar wani ya yi yunkuri taba harkar,
sai a fara cewa zai hana wasu sana'o'insu.

Kwarai fim sana'a ce! Amma wacce iri???

Idan muka kwatanta dabi'un gidajen aure a yau;
da kuma abin dake wakana a gidajen Hausawa,
sannan mu waiwaici baya kafin yawaitar fina-
finan Hausa, za mu iske babu hauragiya da
baranbarama a gidajen aure.

Domin a baya mafi
yawan auren da ake yi ana gina su ne kan
kyawawan al'adun Hausawa, ta yadda za a hori
mace da yin abaibai masu kyaiu koda mijinta ya
munana mata.

Sannan tana da yan fira, wato
yara mata wadanda ke zuwa domin debe mata
kewa, yayin da tatsuniya ta zame musu
makarantun daukar darusa da kaifafa tunani.

A
wancan lokacin, babu batsa da harkokin
sharholiya a cikin tatsuniya ko sauran dangogin
hanyoyin tarbiyyantar da al'umma, musamman
sauran al'amuran da suke kunshe cikin taskar
Adabin Bahaushe.

Mu dawo yanzu, za mu iske rayuwa ta sauya,
inda da yawa gidaddaji suka zama tamkar filayen
dambe da kokawa, ko guraren masha'a da rashin
tarbiyya, kamar tasha ko bariki. Za ku yarda da di
idan na ambata muku cewar mafi yawan
wadannan munanan halaye, sun samu ne
sakamakon tasirin wasu fina-finan Hausa a
tsakankanin al'umma.

Wannan sai ya haifar da
wani mummunan lamari na rashin tarbiyya a
gidan aure, mace za ta iya zagi ko marin mijinta,
kamar yadda za ta iya zabgawa uwar mijinta
mari, ko ta kuntuma mata ashariya.

Dukkan wani
fim da za a yi, lalle za ka iske yana cike da wasu
illoli koda kuwa masu fim din sun yi da'awar
wa'azantarwa suke yi.

Misali, a fim din Hausa ne
za a nunawa mace yadda za ta ci amanar
mijinta, ko yadda 'ya za ta ha'inci ubanta a yayin
da ya tura ta makaranta; sai ta tafi
karuwancinta, ko kuma yadda alhazan birni ke
lalata 'ya'yan mutane.

Haka zalika, mata sun koyi
rashin godiya ga mazajensu a fina-finai, kamar
yadda suka koyi butulci da hana a yi musu
kishiya ko kakarin hallaka kishiyar ko maigidan
gaba.

Magana ta gaskiya, a yau kam fina-finan Hausa
ba gyara tarbiyya suke ba, face rugurguza
tarbiyyar al'umma, wanda wajibi ne gwamnati ta
san wannan, kuma ta nemi gyara.

Duk wani
shedanci da za ka iske mace ta yi, idan ka
tsananta bincike, a fim ta gani.

Da wannan na
fahimci cewa fina-finan Hausa bai dace su shiga
sahun Adabin Hausa ba, sawa'un na zamani ne
ko waninsa, bal ma kamata ya yi su shiga sahun
adabin da su Auwal G Danbarno ke kira da
ADABIN BARIKI.

Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa kamar haka dadinkowa24.blogspot.com

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don ganin sabbin posting din Mu se ku duba saman website din akwai "Home" sai ku shiga, mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa nayau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com

Idan kana/kina da Labarin daku keson asanarwa da Duniya, ko Tambaya,Shawarwari,Hausa Novels, Nishadantarwa,Ilimantarwa,Ko Neman Sani akan ranakun dazamu cigaba dakawo muku Posting na Hausa Novels da Sauran su, zaku iya tuntubar ma'aikatan mu kuturo da Sunan Ku tareda Addreshin Ku tawannan Email din Officialdadinkowa24@gmail.com kyautane zamuyi muku komai don cigaban Al'ummar Hausa bama bukatar kudinka sai dai idan kaikayi niyyar Turowa don siyan Data Saboda acigaba dayin Posting a Kodayaushe batareda dakatawa ba, Website din Mu bashi da Alaka ta kusa ko tanesa da Wani/Wata Dan Siyasa/'Yar Siyasa afadin Duniya Burin mu shine musamu amincewar Al'umma aika da Gudunmawarka,Labari,Shawara da sauran su a Addreshin mu na email ✉💌📩 officialdadinkowa24@gmail.com

Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri

ALLAH yabar Zumunci Amin√√√

Source By  ©Ibrahim Garba Ibn Nayaya

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: