Tuesday 13 March 2018

Karanta Kaji: Me kuke son in fada game da auren Fatima Ganduje- Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

Tura Wannan Zuwa

Shugaban Hukumar HISBA, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya yi bayani a karon farko a kan auren diyar Gwamnan Jihar Kano, Fatima Ganduje.

Shi dai wannan biki, wanda Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da Bola Ahmed Tinubu suka jagoranta a Kano, ya samu halartar gwamnoni da manyan kasa, sannan kuma an yi shagulgula da yawa wanda wasu suke ganin bai kamata ba.

Mutane suntan tambaya wai ina HISBA take ne ake ta irin wannan biki a Kano.

A cewar Shehim malamin kamar yadda Daily Nigerian ta ruwaito daga shafinsa na facebook, “A ranar Asabar na tafi Jihar Sakkwato da misalin karfe daya na rana jim kadan bayan an kammala daurin auren domin in halarci taron kaddamar da littafin sharhin Iziyya da Dokta Mansur ya wallafa.

“Bayan na yi kwana biyu a Sakkwato, sai na tafi Zamfara domin yin wa’azi, na yi kwana daya a can sai kuma na tafi Kaduna domin gabatar da shiri a gidan Talabijin na DITV na sa’a biyu.

“A ranar Juma’a sai na yi wamata wa’azi a garin Rigasa da ke Kaduna, sannan kuma na yi hudubar juma’a, sannan kuma bayan sallar Magriba sai na yi wa’azi a masallacin marigayi Sheikh Rabiu Daura.

“Da safiyar Asabar sai na kara yi wa wasu matan wa’azi a masallacin Sultan Bello daga nan kuma sai dao Kano. Duk wanda ke son gani na, yanzu na dawo ofis dina.

“Kowa na so ya ji jawabina a kan bikin auren diyar gwamna, me kuke so in fada?

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku
Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Muryarhausa24.com don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum

An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com
Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Muryarhausa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki
daya Amin Summa Amin.

Source by ©Aminiya

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: