Friday 16 March 2018

Karanta Kaji: Nayi Alkawarin Zanyi Lefe Ga duk wanda Zai Aure ni-Hauwa Waraka

Tura Wannan Zuwa
Jarumar fina-finan Hausa, Hauwa Abubakar wacce aka fi sani da Hauwa Waraka, ta ce tana yawan fitowa a mutuniyar banza ne saboda ta nunawa al'umma illar rashin kirki.

"Ina fitowa a matsayin karuwa ko 'yar kwaya ko ballagaza ne saboda na ilimantar da mutane domin su guji zama irin wadannan mutane", in ji Hauwa Waraka, a hira ta musamman da BBC.

Ta kara da cewa, "Ban taba karuwanci ba kuma ban taba yin hulda da karuwai ba, amma idan ina taka rawa a matsayin karuwa kai ka ce ni tsohuwar magajiya ce."

A cewar jarumar bai kamata mace da za ta fito a matsayin karuwa "a gan ta sanye da hijabi ba. Ko kuma macen da ta fito a matsayin 'yar shaye-shaye a gan ta ras kamar mutuniyar kirki ba.

"Shi ya sa za ka gan ni ina keta rashin mutunci a fim kamar da gaske. Kuma abin da ya kamata kenan."

Hauwa Waraka ta ce sau da dama tana zuwa unguwa mutane suna "cewa wacce irin kwaya ko wiwi ko taba za su kawo min na sha. Ba su san cewa ban taba shan kayan maye ba; wallahi ko taba ban taba sha ba. Duk abin da ka ga ni a fim ne".

Da aka tambaye ta kan zargin da ake yi wa 'yan fim na luwadi da madigo, jarumar ta ce akwai bara-gurbi sosai a cikinsu "kamar yadda akwai su a cikin ko da Malaman addini amma bai kamata a yi mana kudin-goro ba."

Ta bukaci mutane su rika yi musu uzuri musamman ganin cewa su ma mutane ne kamar kowa.

Hauwa Waraka, wacce ta ce tana son yin aure, ta kara da cewa "kai ma wakilin BBC idan kana sona ka fito. Wallahi aurena ba zai yi tsada ba. Kai, ni zan hada maka lefe ma akwati shida idan kana so.

"Ko da yake na san tsoron matarka kake yi kada ka je gida ta ki bude maka kofa"...(dariya).

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku
Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Muryarhausa24.com don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum

An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com

Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Muryarhausa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu
Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki
daya Amin Summa Amin.

Source by ©Bbc Hausa
TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user