Friday 6 April 2018

Karanta Kaji: Zan Auri Daya daga cikin 'yan Hausa Film Ku Tayani da Addu'a- Sheikh Isa Alolo

Tura Wannan Zuwa

A hira da PREMIUM TIMES HAUSA tayi da shahararren dan wasan fina-finan Hausa, furodusa kuma mai ba da umarni, wato darekta Sheikh Isa Alolo daga Abuja, Jarumin ya bayyana wa jaridar dalilan da ya sa ya tsunduma cikin harkar shirya fina-finan Hausa.

Bayan haka ya fadi mana irin mace da yake shirin ya aura, kuma kila ma ‘yar gida za a yi in Allah ya yarda.

PT: Kowa dai yasan cewa malami ne ake yi wa lakani da Sheikh, Yaya akayi ka samu naka sheikh din, ko dama can shehi ne?

Sheikh: A’a ni dai musulmi ne na kwarai sannan mai kula da addinin sa. Ina iya kokari na wajen ganin duk abin da na sa a gaba na kan yi kokari in ga nayi fice akai. A haka a haka ne har aka rada mini wannan lakani.

PT: Yaya kake ji idan aka kira ka da wannan suna?

Sheikh: Ji nake kamar wan shugaban kasa, tun da suna ne mai kyau. Ina jin dadin haka.

PT: Yaya akayi ka fara harkar fina-finai?

Sheikh: Tun Ina yaro nake sha’awar shiga harkar fim, kamar yadda duk wani akto ke fadi amma sai dai nawa da dan bambamci domin na fara da yin kwalliya ne daga nan sai na fara yin gaba-gaba har na kawo inda nake yanzu.

PT: Ina kake yanzu?

Sheikh: Ni yanzu akto ne, furodusa, kuma darekta.

PT: Ba ka ganin aiki zai iya maka yawa, ganin wadannan abubuwa da aka ambato duk suna bukatar maida hankali?

Sheikh: Haka ne, sai dai yanzu na fi maida hankali ne wajen harkar darektin.

PT: To yaya maganar harkar kwalliya?

Sheikh: Bana yin kwalliya yanzu, sai dai na kan dan leka sama-sama, amma bashi nake yi ba.

PT: Fim nawa ka yi zuwa yanzu?

Sheikh: Gaskiya bazan iya tunawa ba yanzu, amma na san tabbas ya wuce 100.

PT: Wanne ne yafi baka wahala?

Sheikh: ‘KIJE KYA GANI’, bazan taba mantawa da wannan fim din ba. Na yi matukar wahala a wannan fim. Bayan makudan kudi da na kashe a fim din, a wannan karo ne na fara fita daga kano domin zuwa wuraren da zan yi amfani dasu wajen yin fim din. A haka ma an yi ta kai ruwa rana sannan kuma mun sha tsananin wahala. Bayan haka ba karamin hasara nayi ba.

Fim din bai yi kasuwa ba kwata-kwata. Kai a lokacin saura kadan in hakura da harkar fina-finai.

PT: Wani fim ne ya fi faranta maka rai?

Sheikh: ‘UWAR GULMA’ Wannan fim yayi min dadi, fim ne da komai da nayi a fim din ya karbu. Na shana sosai da wannan fim din. Abin dai Allah ne ya saka min da wahalar da na sha a wancan lokacin da hakuri da nayi.

PT: Kana sha’awar fitowa a fina-finai na barkwanci, me ya sa haka?

Sheikh: Ina da shawa’ar sa mutane nishadi, shine ya sa nake son haka. Ina so in ga mutane cikin farin ciki a ko wani lokaci, shine ya sa nake fitowa a irin wadannan fim din.

PT: ko kayi aure?

Sheikh: A’a, bani da mata sai dai ina kokarin ganin na yi aure nan ba da dadewa ba, kuma ina ganin ‘yar gida nake sa ran za a yi, wato kila ma taurariyar Kannywood ce. Sai dai kun gani.

Daga karshe ina so inyi amfani da wannan dama domin jinjinawa gidan jaridar PREMIUM TIMES da kokari da take yin a yada ayyukan mu a kannywood. Muna godiya.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku
Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Muryarhausa24.com don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum

An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com
Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Muryarhausa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki
daya Amin Summa Amin.

Source by ©Fim Hausa

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: