Thursday 5 April 2018

Kalli Yadda Za a bude gidajen Kallo sinima na farko a kasa Mai Tsarki Saudiyya

Tura Wannan Zuwa

A karon farko cikin shekara 35 za a bude gidan sinima na farko a kasar Saudiyya a ranar 18 ga watan Afrilu.

Abin da zai share fagen bude wadansu gidajen sinimar kusan 100 a fadin kasar nan da shekarar 2030.
A baya dai a shekarun 1970 akwai gidajen sinima, a kasar, amma kuma aka rufe su saboda maganganu da tasirin malaman addinin Musulunci da ke daular.

Tun bayan da hukumomin Saudiyyar suka sanar kimanin watanni hudu da suka gabata cewa za a sake bude gidajen sinima a kasar bayan kusan shekara 40 da rufe su, abubuwa sun gudana cikin gaggawa na tabbatar wannan alkawari.
Ranar 18 ga wannan wata na Afrilu, ita ce Saudiyyar ta sa domin bude kofar sinimar ta farko a babban birnin kasar, Riyadh.

Hakan na daga yarjejeniyar da kasar ta kulla da babban kamfanin gidajen sinima na duniya AMC, inda a karkashin shirin zai bude gidajen sinima 40 a biranen Saudiyyar daban-daban a cikin shekara biyar nan gaba.

A shekarar data wuce hukumomin na Saudiyya sun dukufa sosai wajen shigar da harkoki nishadi kasar, a matsayin wani muhimmin mataki na bunkasa kasar nan da shekara ta 2030, mai taken Vision 2030.

Wato shirin aiwatar da sauye-sauye na tattalin arziki da zamantakewa wanda Yarima mai-jiran-gado Mohammed Bin Salman, wanda yanzu yake Amurka wajen gayyato masu zuba jari a kasar, ya bullo da shi.

Shiri ne wanda kasar ta bullo da shi domin fadada tattalin arzikinta ta yadda za ta kauce daga dogaro da mai, tare da samar da sabbin ayyuka da kuma samar da hanyoyin da 'yan kasar za su rika zama suna kashe kudadensu a gida, maimakon fita kasashen waje.

Ana sa ran zuwa shekara ta 2030 za a samu gidajen sinima kusan 100 a kasar, wanda wannan shiri ne da zai kasance wani abin maraba ga 'yan kasar da ke da sha'awar zuwa gidajen sinima.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku
Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Muryarhausa24.com don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum

An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com
Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Muryarhausa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki
daya Amin Summa Amin.

Source by ©Bbc Hausa

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: