Saturday 19 May 2018

Kalli Sabbin Hotunan Shugaban Nigeria Buhari dasu Janyo Cece-Kuce a Shafukan Sada Zumunta - Bude Ku Kalle su Ku sha Mamaki

Tura Wannan Zuwa

'Yan Najeriya suna ci gaba da bayyana ra'ayoyinsu game da wani hoton Shugaban Kasar Muhammadu Buhari da aka wallafa lokacin da ya halarci tafsirin Al-Kur'ani a fadarsa da ke Abuja.

A ranar Alhamis, wato ranar farko ta fara azumin watan Ramadan, fadar shugaban ta yada hoton a shafukan sada zumunta.
BBC ta samu dimbin ra'ayoyin jama'a a shafukanmu na sada zumunta bayan wallafa hoton musamman a shafinmu na Facebook.

Wasu 'yan kasar sun bayyana halartar tafsirin da cewa siyasa ce kawai, ganin cewa zabe ya karato kuma shugaban na neman wa'adi na biyu.

Yayin da magoya bayan shugaban suke kare halartar tasa, suna masu yaba masa da kuma yi masa addu'ar samun nasara da karin lafiya.

Adams Babangida cewa ya yi:

"Ko me yake saurare oho... A gaya masa gidajen talakawa da yawa yanzu haka an sha ruwa ba su da abin kai wa baki, sakamakon irin tashin gauran zabi da abubuwan masarufi suka yi kawai don an cire talafin da a baya yake talafa wa talakawan."

Hakazalika shi ma Frankling Auwal nuna damuwarsa ya yi game da halin da talakawan kasar suke ciki:

"Ina ruwan talaka da jin tafsirin shi, ya sauke nauyin mutane da ke kan shi, talaka bai zabe shi ba don a nuno shi ya je tafsir ba."

Amma Hassan Muhammad shi nuna farin cikinsa ya yi dangane da batun:

"Alhamdulillah wannan irin abin farin ciki da ba zai misaltuba. Ga shugaban kasata yana sauraron tafsir. Allah Ya kara maka lafiya. Allah Ya baka ikon ci gaba da ayyukan alheri. Mun gode da ganinka a cikin wannan yanayi mai ban sha'awa."

Wani dan jarida a kasar Abdulaziz Abdulaziz shi ma ya bayyana ra'ayinsa dangane da batun kamar haka:

Jama’a a taya ni dubawa. Wai su malaman Villa ko tafsirin nan ba kakkautawa suke yi ne, bana azumi ba kawai? Na ga daga...

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin aiki Tukuru don jin dadin ku Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin website din akwai "Home" sai ku shiga,

mungode

Muryarhausa24.com Zata Kasance Babbar Kafar Yada Labarai aduk fadin Duniya domin Bunkasa Harshen Hausa, domin Zafafan Labarai ziyarci www.muryarhausa24.com

Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com

Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin Muryarhausa24.com aduk inda kuke a fadin Duniya farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24.com shine ta fito da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi
me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@
gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki daya Amin

Source by ©BBC HAUSA

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: