Wednesday 9 May 2018

Karanta Kaji Dalilin sa: Ina so gwamnatin Buhari ta gina manyan sinimomi a Arewacin kasar Nigeria - Darakta Kamal S. Alkali

Tura Wannan Zuwa
Fitaccen daraktan fina-finan Hausa, Kamal Sani Alkali ya ce abubuwan da yake so Buhari ya yi wa masu shirya fina-finan Hausa na Kannywood su ne, ya sanya gwamnatin tarayya ta samar da tsare-tsare na musamman da za su sanya masana’antar ta rika samun ci gaba mai dorewa.

Daraktan, wanda shi ne shugaban Kamfanin Kamal International Limited mai babban ofishinsa a Kano ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake tattaunawa da wakilin Aminiya ta wayar tarho.

Alkali wanda ya bada umarni a manyan fina-finai da suka hada da ‘Umar Sanda’ da ‘Sahabi’ da kuma ‘Guguwar So’ ya ce, rashin isasshen jari a wurin ’yan fim da karanci sinimomi da kuma matsalar satar fasaha ne suka hana Kannywood bunkasar a-zo-a-gani, inda a yanzu masana’antar take cikin wani hali.

Ya ce, “Ina so gwamnatin Buhari ta gina manyan sinimomi a Arewacin kasar nan, sannan ta ba ’yan fim bashin da babu kudin ruwa a cikinsa, ko tallafa wa ’yan fim da jari, ko dai ta ba su bashin da babu kudin ruwa a cikinsa don su gina sinimomin a Arewa.

“Idan gwamnatin Buhari ta yi hakan, to Kannywood za ta bunkasa, bunkasar da za ta sa ta rika gogayya da manya-manyan masana’antun fina-finai na duniya,” inji Kamal.

Daraktan wanda ya lashe Gwarzon Darakta yayin Gasar City People Entertainment ta 2017 ya kuma bukaci gwamnatin Buhari ta samar da ingantacciyar hanyar yaki da masu satar fasaha ko barayin zaune da suka addabi masana’antar fiye da shekara 15.

Ya ce, “Kannywood tana cikin ta mawuyacin hali, zan iya cewa ta kusa durkushewa saboda masu satar fasaha da barayin zaune. Kada a manta kafin kowane fim ya fita sai an biya Hukamar Kare Hakkin Mallaka ta kasa Naira dubu 15, sannan a biya Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano Naira dubu 10 da dari 500, amma hukumomi sun kasa samar da nagartacciyar hanyar yaki da masu satar fasaha.”

Alkali wanda ya tsara labaran fina-finai irinsu, ‘Jarumin Maza’ da ‘Gaba Da Gabanta’ ya kuma shawarci gwamnatin tarayya da ta zuba jari a masana’antar don ganin an samar da fina-finai masu inganci.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com

Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki 

Mungode

Source: Hausa Mini

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user