Wednesday 10 October 2018

Karanta Kaji: Dalilai 5 da Yasa Gwamnatin America ta Hana Atiku Abubakar shiga cikin Kasar America - Yakamata Kusan Dalilan nan

Tura Wannan Zuwa
Wani kwamiti da kan tsaron cikin gida da harkokin gwamnati da kasar Amurka ta kafa, ya fitar da wani rahoto, wanda ya zayyana mutane 4 da suka zama manyan barayi a kasashen Afrika, da ke aikata manyan badakaloli ta hada hadar kudade ba bisa ka'ida a kasashen turai, musamman a Amurka.


Kwamitin ya fara bincike kan hada hadar kudade da Atiku ya ke yi a kasar ta Amurka, tare da fara rubuta wannan rahoton nasa a ranar 4 ga watan Febreru, 2010. Kwamitin ya zayyana badakaloli 5 da Atiku ya aikata na hada hadar kudade a kasar Amurka ba bisa ka'ida ba.

1. Atiku Abubakar ya yi amfani da matarsa ta 4, Jennifer Douglas, yar asalin kasar Amurka, wajen shigar da $40m zuwa cikin kasar Amurka, kudin da ake zargin an sace su ne a tsakanin shekarar 2000 zuwa 2008. Kudaden sun hada da cin hancin $1.7m daga kamfanin Sieman AG, da ke da matsugunni a Jamus, da juma $38m daga wasu kamfanonin kasashen waje, musamman kamfanin LetsGo Ltd. Inc., Guernsey Trust Company Nigeria Ltd., da kuma Sima Holding Company.

2. Ms. Douglas ta taimakawa Atiku wajen ganin kamfanonin kasashen wajen sun tura kudaden da suka kai akalla $25m a wasu bankuna daban daban na Amurka ta hanyar yanar gizo. Tsawon lokaci bankunan Amurkan basu san daga ina Douglas ke samo wadannan makudan kudade da take ajiyewa. Ganin bankunan sun fara zarginta, Ms Douglas ta soma bude asusun bankuna da sunayen gidauniya, ciki akwai gidauniyar Gede da ta kafa a 2002, sai kuma ta raba kudin ga jami'ar Amurka a Nigeria (AUN) da Atiku ya kafa a 2003, da sauran wasu kungiyoyin taimakon al'umma da ta kafa a kasashe daban daban, duk don boye kudaden.

3. Lauyan Ms. Douglas, Mr Abubakar da kuma jami'ar Azuzn a Amurka, Mr. Weidenfeld ya yi rawa ya yi tsaki akan wani bincike da bankunan Amurka suka soma yi kan $14m da wasu boyayyun kamfanoni suka tura da sunan jami'ar AUN. Ya ce Atiku na turo kudin ne don biyan kudaden hakkokin ma'aikatan jami'ar da kuma harajin kasar Amurka da sauran bukatu.

4. A 'yan shekarunnan, bincike ya fara tsananta kan hanyoyin da Atiku ke samun wadannan makudan kudade. Sanin kowa ne ya shafe shekaru 20 a hukumar hana fasa kwabri ta kasa (Kwastam), kuma ya yi aiki a kamfanoni masu zaman kansu na tsawon shekaru 10, kafin daga bisani ya zama mataimakin shugaban kasar Nigeria daga 1999 zuwa 2007. A lokacin da ya ke mataimakin shugaban kasa, Atiku ne ake zargi da kwashe kudi daga gidauniyar fasahar man fetur ta kasa NPTD.

5. A watan Disambar 2008, hukumar tsaro da canjin kudi ta Amurka, ta zargi waji kamfani mai suna Seimens AG, da ke da zama a Jamus, cewar a 2001 da 2002, ya tura akalla $2.8m a matsayin cin hanci ga wasu bankuna da Ms Douglas ta ke da asusun ajiyar kudi a ciki, a cikjn wani yunkuri na baiwa wasu 'yan Nigeria cin hanci. Kamfanin Seimens ya amince da wannan zargi na tura wadannan makudan kudade ta yanar gizo don baiwa kamfanini da jama'a cin hanci, inda ya biya tarar $1.6bn ga kasar Amurka akan aikata wannan laifi.

Sai dai Ms. Douglas ta karyata duk wani zargi da ake mata, amma kwamitin binciken ya bankado wasu bayanan musayar kudade da ke nuni da cewa Ms Douglas ta tura sama da $1.7m daga kamfanin Seimans AG zuwa asusunta na Ms. Douglas da ke Citibank.

Karanta Kaji:Abubuwan da Yakamata Kusani dangane da Siyasar Buhari da Atiku a 2019

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: Hausa Naij
TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user