Thursday 20 December 2018

Takaitaccen Tarihin Jamhoriyar Kasar Niger: Abubuwan da Yakamata ku Sani Dangane da Kasar Nijar

Tura Wannan Zuwa Ga
Jamhuriyar Nijar ta samo sunan ta ne daga kogin Naija duk kuwa da cewa ba ta kusa da wata babban mashigin ruwa. Nijar na makwabtaka da Najeriya da Benin ta kudanci, Burkina Faso da Mali ta yammaci, Aljeriya da Libiya ta arewaci, sai kasar Chadi ta bangaren gabas.



Kodayake sai a cikin karni na goma sha tara ne Turawa kamar Mungo Park dan kasar Burtaniya, suka fara shiga can bangaren kogin Naija, to amma dai tun kafin wannan lokacin Faransa ke ta kokarin ganin ta mallaki Nijar, inda ta samu nasara a shekarar 1890.

A wannan lokaci Faransa ta na da gwamnonin dake tafiyar da harkokin dukkanin yankunan da ta mamaye a yammacin Afirka ciki harda Nijar, wadanda ke aiki karkashin babban gwamna, wanda ke zaune a Dakar na kasar Senegal.

Ranar goma sha takwas ga watan Disambar shekarar 1958, Niger ta zamo Jumhuriya mai cin gashin kanta a karkashin ikon Faransa.
Sannan a ranar uku ga watan Agusta na 1960, jamhuriyar Nijar ta samu 'yancin kai, wato shekaru hamsin da suka wuce.



Kalubale

Jamhuriyar Nijar ta yi fama da juyin mulki daga sojoji daban daban wadanda suka mamaye madafen iko a kasar bayan ta samu 'yancin kai.
Kasar wacce ke fama da matsanancin fari, na fadi-tashin ciyar da jama'arta.

Babban abin da take fitarwa dai shi ne ma'adanin Uranium wanda shi ma a shekarun baya ya fuskanci rashin tabbacin farashi, yayin da kwararowar hamada ke barazana ga aikin noma.

Amma a gefe guda kasar na fatan fara hako man fetur wanda ka iya bunkasa tattalin arzikinta.

Bayan samun 'yancin kai, kasar ta fuskanci mummunan fari wanda ya lalata albarkatun noma.

Kasar dai ba ta da wani tsarin ilimin Firamare na azo a gani, abin da ya sa take cikin jerin kasashen da ke fama da rashin ingantaccen ilimi a duniya.

Harkar lafiya ma ba ta da kyau sosai, kuma akwai yaduwar cututtuka a ko'ina cikin kasar.

A lokuta da dama kasar ta yi fama da boren 'yan tawayen Abzinawa a Arewacin kasar.
Sai dai a shekara ta 2009, gwamnati da 'yan tawayen sun sanya hannu kan yarjejeniyar samar da zaman lafiya a birnin Tripoli na kasar Libya.

Shugaban mulkin soji: Salou Djibo

An bayyana babban jami'in soji Salou Djibo, a matsayin shugaban gwamnatin sojin kasar, bayan da sojoji suka hambaras da gwamnatin shugaba Mamadou Tandja a watan Fabrairun shekara ta 2010.

Jami'an sojin sun yi alkawarin mayar da kasar kan tafarkin dimokradiyya, sannan suka nada Fira minista farars hula Dr Mahamadou Danda, a matsayin shugaban gwamnati.

Hukumomin sun kuma haramtawa kansu da kuma jami'an gwamnatin rikon kwariya, shiga harkokin zaben kasar.

Juyin mulkin ya sa Tarayyar Afrika ta dakatar da kasar daga kungiyar, sai dai kasashen duniya sun yi taka tsantsan wajen Allah wadai da matakin da sojojin suka dauka, inda suka neme su da su maida kasar kan tafarkin dimokradiyya.

An haifi shugaba Janar Salou Djibo a shekarar 1965 a Arewacin yankin Tillaberi.

Ya samu horon soji a kasashen Ivory Cost da China da Morocco, sannan ya yi aiki da tawagar sojin kasar da ta yi aikin kiyaye zaman lafiya karkashin Majalisar Dinkin Duniya a kasashen Ivory Cost da jamhuriyar Congo.




Kafafen yada labarai

Gwamnati ce ke da mallakin kusan baki dayan kafafen yada labaran kasar, sai dai a 'yan shekarun nan an samu karuwar kafafen yada labarai masu zaman kansu.


Kafar Rediyo ita ce hanya mafi sauki da girma ta samun labarai a Nijar, akwai kuma jaridu na gwamnati da masu zaman kansu.

Gidan Radiyon Faransa na watsa shirinsa ta tashar FM a biranen Yamai da Maradi da kuma Zindar. Haka kuma ana kama BBC a zangon FM a gidajen rediyo masu zaman kansu da dama.


Akwai kuma masu amfani da hanyar sadarwa ta Intanet kimanin dubu tamanin a watan Yuni na shekara ta 2009.


Adadin jama'a

Kidayar jama'ar da aka gudanar a shekara ta 2009 a Nijar, ta nuna cewa yawan jama'ar kasar ya haura miliyan goma sha biyar.

Kidayar ta kuma nuwa cewa kashi tamanin da daya cikin dari na jama'ar kasar na zaune a yankunan karkara ne. Duk da arzikin albarkatun kasar da Allah ya yiwa Nijar, kimanin kashi sittin da biyar cikin dari na jama'ar kasar na rayuwa kan kasa da dalar Amurka daya, kwatankwacin kudin CFA 530 a rana (Watch Fluctuation na canji dala).

Batun cin hanci da rashawa da ake zargin shugabannin kasar na yi na taka rawar gani a halin talaucin da kasar Nijar ke ci gaba da fuskanta.

Fannin ilimi

A Jumhuriyar Nijar, tilas ne a ba kowanne yaro mace ko namiji mai shekaru shidda ilimin Firamare. Sai dai kuma yaran da ake sawa a makarantun Firamaren ba su da yawa musaman ma dai 'ya 'ya mata. kimanin kashi sittin cikin dari na yaran da suke kammala aji shida a Firamare maza ne, inda a yawancin lokuta ake tura yaran aiki a maimakon zuwa makaranta, musamman a lokutan damina.
Haka kuma akwai yaran makiyaya wadanda ba su da takamaiman matsuguni, ballantana makarantu.

Fannin Lafiya

Bangaren kiwon lafiya na da matukar rauni a jamhuriyar Nijar, dalilin da ya sa kasar take kan gaba cikin jerin kasashen da aka fi samun yawan mutuwar kananan yara a kasashen da ke makwabtaka da ita, musamman sabili da rashin ingantaccen abinci mai gina jiki da yaran ba sa samu.

A cewar kungiyar kare kananan yara ta Save the Children, Nijar ita ta fi kowace kasa a duniya yawan mace- macen kananan yara.
Har ila yau kasar na fama da yawan mutuwar mata masu juna biyu lokacin haihuwa.

Zirga zirga

Batun zirga- zirga na da muhimmancin gaske ga tattalin arzikin Nijar, inda hamada da manyan tsaunuka suka rarraba yankunan kasar musamman ta Arewaci.

Tun asali, babbar hanyar zirga- zirga a Nijar ita ce ta rakuma da wasu dabbobi ko bisashe kuma a wasu wuraren kamar kudanci da yammaci a kan yi amfani da 'yan abubuwan da ake da su ta ruwa da ba su da yawa.

Kuma hakan bai sauya ba ko lokacin mulkin Turawa. Har yanzu dai babu hanyar dogo ko jirgin kasa kuma ko kwalta babu a titunan da ake da su a lokacin mulkin Turawa.

Bayan da kasar ta samu 'yancin kai, sannu a hankali an samu manyan tituna da ake yawan zirga -zirga ta kananan motoci ko tasi, safa safa da manyan motocin daukar kaya.

Babban filin jirgin saman kasar shi ne na Diori Hammani dake a birnin Niamey. Akwai kuma wasu manyan filayen jirgin saman a Agadez da Zinder.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: BBC HAUSA

TURA WANNAN ZUWA GA

Mawallafi: verified_user