Friday 25 January 2019

Karanta Kaji: Kuskure 3 da akai a cikin Film din MATAR MIJINA tare da Sharhin Fim din

Tura Wannan Zuwa
Suna: Matar Mijina
Tsara Labari: Nazir Alkanawi
Kamfani: S.H Ea: Abdul Amart
Umarni: Sadik N. Mafia


Matar Mijina


 Jarumai: Adam A. Zango. Aisha Aliyu Tsamiya, Fati Washa, Umar Gombe, Maryam Ceeter. Da sauran su.

 A farkon fim din an nuna Mutallab (Adam A. Zango) Yana bacci a cikin daki yayin da ‘ya’yan sa Yusra da Salim suka shiga suka tashe sa don yayi Karin kumallo. Bayan Mutallab ya tashi ya kimtsa ne ya fita wajen aikin sa, a sannan ne Suwaiba (Maryam Ceeter) tazo wajen Matar sa wadda ta kasance kawa ce a wajen Suwaiba. Suwaiba ta kasance tana nuna wa Jalila (Aisha Aliyu Tsamiya) aibun auren da tayi gami da ajiye karatun tan a jami’a ta zabi aure, yayin da Jalila take nuna mata hakan ba laifi bane saboda tana jin dadin irin soyayyar da mijin ta Mutallab yake nuna mata. Suwaiba tana kokarin zuga Jalila don kada ta cigaba das akin jiki da mijin ta Mutallab saboda gudun kada ya karo mata kishiya, amma Jalila tana nuna ko da hakan ta kasance ba laifi bane zata iya zama da kowacce mace wadda mijin ta zai aura. Wata rana Mutallab ya hadu da wata budurwa Samira (Fati Washa) wadda yaji ta birge shi kuma yana son auren ta, hakan ne yasa ya fara nuna wa Samira kudurin san a son auren sa kuma cikin dan lokaci kadan Samira ta amince da bukatar sa suka fara soyayya. Mutallab ya sanar da matar sa Jalila cewar yana soyayya da Samira sai hakan bai dameta bat a nuna masa goyon bayan ta akan auren da zai kara, har ya zamana cewa Mutallab yakan hada Jalila da Samira a waya su gaisa har ma suyi hira, sannan kuma yakan dauki ‘ya’yan sa Yusra da Salim ya kais u wajen Samira su gaisa. Tun Samira tana ja baya da Jalila hart a saki jiki da ita kuma ta fahimci cewa Jalila mace ce mai son zaman lafiya wadda kuma bata damu da soyayyar da ake yi da mijin taba. Wata rana Suwaiba kawar Jalila ta fito tare da kawayen ta daga cikin makaranta sai taga Mutallab ya budewa Samira motar sa yaja sun tafi, hakan ne ya kidima tat a garzayo ta sanar da kawarta Jalila abinda idanun ta suka gani, amma sai Jalila ta nuna rashin damuwar ta akan abin duk da Suwaiba ta nuna mata cewar yarinyar da ta gani tare da Mutallab bata da nutsuwa, amma yardar da Jalila tayi da mijin ta itace tasa ta gamsu da cewar ba zai ci amanar taba. Cikin dan lokaci kadan aka bikin Mutallab da Samira ya gabato, wanda hakan yasa Jalila ta soma gayyatar jama’a da sauran dangin ta har ma ta fidda kalar ankon da za su saka ranar biki. Hakan ne yasa wasu daga cikin ‘yan uwan ta suke kokarin zuga ta don kart a amince da hakan, yayin da wasu dangin nata kuma suka yi fushi da ita suke ganin kamar bata da hankali saboda tana murna don za’a yi mata kishiya. Ana ya gobe daurin aure sai Mutallab yayiwa Jalila sallama ya koma dakin hotel tare da abokan sa don su samu sakewa saboda baya son hayaniyar jama’a ‘yan biki. Kwatsam ana tsaka da shagalin biki sai ga Suwaiba kawar Jalila ta zo ta tabbatar mata da cewar Samira amaryar da za’a kawo mata tana dauke da cutar kanjamau, saboda abokin tan a makaranta wanda ake zargin tana mu’amula dashi an gane cewar yana dauke da wannan cutar. Jin hakan ne ya tashi hankalin Jalila ta kira mijin tat a nuna kada a daura wannan auren, amma sai Mutallab yayi zaton cewa kishi take da abin sai yaki saurarar ta. Sai dai kuma tun bayan auren Samira da Mutallab sai Jalila taja jikin ta gefe ta daina mu’amula da mijin ta, sannan kuma taki amincewa akan ya kusance ta saboda tana ganain cewa shima ya kamu da wannan cuta ta kanjamau. Hakan ne yasa ko ya kwana a kan gadon ta sai ta cire shimfidar gadon ta kona saboda kyankyamin sad a take yi. Ganin abinda ke faruwa ne yasa Mutallab ya soma nadamar karin auren da yayi saboda baya son abinda ke faruwa tsakanin sad a Jalila. Hakan ne yasa ya kira iyayen Jalila don su tuhume ta akan abubuwan da take yi masa, a sannan ne Jalila ta basu labarin abinda Suwaiba kawarta ta gaya mata, jin hakan ne kuma yasa Samira ta karyata cewar tana dauke da cutar kanjamau, wannan daalilin ne kuma yasa aka je asibiti akayi gwaji wanda ya tabbatar da cewa Samira da Mutallab bas u da wannan cuta ta kanjamau. Faruwar hakan c eta sa Jalila tayi nadama kuma ta roki gafarar mijin tad a ta Samira, wanda hakan yasa lokacin da Suwaiba ta sake zuwa gidan suka hadu gaba daya sukayi mata duka don kokarin kawo karshen munafurcin ta.

 Abubuwan Birgewa:

 Labarin ya tafi kai tsaye har ya adire bai karye ba.

Sunan fim din ya dace da labarin.

 Daraktan yayi kokari wajen tafiyar da labarin ta hanyar da ta dace, haka kuma yayi kokari wajen ganin cewa jaruman sun isar da sakon da ya dace, domin sun yi kokari wajen isar da sakon da ya dace. Hoto ya fita sosai, haka ma sauti ba laifi.

   Kurakurai:

 Bayan auren Mutallab (Adam A. Zango) da amaryar sa Samira (Fati Washa) me kallo ya gan su a wani falo na daban wanda bai yi kama da gidan sa da aka fara bayyanawa a fim din ba, sannan kuma yanayin da aka nuna kamar dama a gidan suke, shin canja gida suka yi? Idan kuma gidan bangare biyu ne to ya kamata tun a farko a bayyanawa me kallo, duk da dai yanayin yadda aka bayyana tsarin gidan a baya bai yi kama da cewar bangare biyu bane.

Lokacin da Jalila (Aisha Tsamiya) ta sami labarin cewa amaryar da mijin ta zai aura tana dauke da cutar kanjamau, me kallo yaga tana guje masa domin ko zama a inda yake bat a yi, wanda bayan ya kwanta akan shimfidar ta ma sai ta kona zanin gadon duk da shima zanin gadon bata taba shi da hannu ba har sai da ta sa leda ta rufe hannuwan nata, sannan ta dauka ta kona, shin Jalila ba ta san cewa ba a daaukar cutar kanjamau ta hanyar zaman takewa da masu cutar ba? Tun da an nuna cewar tana da ilimin addini da na zamani gami da fahimta, bai dace kuma a nuna cewar ta kona shimfidar da mijin ta ya kwanta ba don gudun kamuwa da cutar da take zargin sad a ita.

Lokacin da Jalila ta fara fadawa kawarta Suwaiba labarin cewa mijin ta zai kara aure, bayan tafiyar Suwaiba me kallo yaji muryar ta a waya sa’in da ta kira Jalila tana sanar da ita cewar yarinyar da mijin ta zai aura tana saka hotunan sa Instagram, haka zata zuba idanu bazata dau mataki ba, shin ya akayi Suwaiba ta gane cewar amaryar da za’a auro tana saka hotunan Mutallab a Instagram alhalin a sannan bat a san sunan tab a kuma bata ga ma hoton tab a balantana ayi zaton ko a sannan ta san ta? Ya dace a samar da dalili kafin faruwar hakan. 

Karkarewa:

Fim din ya fadakar domin an nuna illar daukar zugar kawaye tare da kuma illa ga budurwa mai sakin jiki da maza a waje wanda hakan yakan ja mata mugun zargi.

Haka kuma an nuna darasi ga wasu matan ta hanyar nuna musu ba laifi bane don mijin su zai kara aure. Wallahu a’alamu!



Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: Leadership Hausa


TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user