Saturday 18 April 2020

Ya Matsayin Kudin Da Aka Tarawa Mara Lafiya Don Neman Magani Sai Ya Rasu?

Tura Wannan Zuwa
TAMBAYA

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Wa Barakatuh. malam Dan Allah a warware mana wannan matsalar.

YA MATSAYIN KUƊIN DA AKA TARA WA MARA LAFIYA DON NEMAN MAGANI SAI YA RASU...

Mutum ne ba lafiya aka nema masa taimakon kuɗi domin dashen ƙoda, ana cikin haka ba'a kai ga gamawa ba sai ya rasu to wannan kuɗin nasa ne ma'ana yazama nashi  zai shiga gadonshi ko za'a iya taimakon wani mai tsananin buƙata irin wannan larurar?? Mun gode jazakumullahu khairan.

AMSA

Wa'alaykumussalam

Dukiyar da wani ya bayar don mamaci, kafin ko a bayan rasuwar sa ne, ita ma ta na cikin dukiyar gado.

A duba : [FATA'WAL LAJNATID DA'IMA; 16/473]

Wallahu A'alam

AMSAWA: Malam Nuruddeen Muhammad (Mujaheed)

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: