Friday 1 December 2017

HUKUNCIN SANYA TUFAFIN ARNA A GARURUWANSU-Ibrahim na yaya

Tura Wannan Zuwa

Lallai abu ne sananne saba wa Kafirai da
Mushrikai a abubuwa na rayuwa da suka kebanta
da su yana daga cikin manufofin Shari'ar
Muslunci.

Shi ya sa aka samu hadisai masu yawa
sun zo suna umurtanmu da saba wa Yahudu da
Nasara a siffofinsu na zahiri, na Tufafi da Al'adu
da sauran lamura na rayuwa, kuma suka hana
mu kamanceceniya da su da kwaikwayonsu.

Amma sai dai saba musun yana kasancewa ne a
lokacin karfi da izzan Musulmai. Amma duk inda
Musulmai suke da rauni to saba musun ba wajibi
ko mustahabbi ba ne, matukar zai haifar da
cutarwa.

Don haka duk lokacin da Musulmai suka kasance
a garuruwan kafirai da kasashensu, to babu
bukatar su saba musu, don tsoron cutarwa.

Kai,
kamantuwa da kafiran a siffofinsu na zahiri,
kamar tufafi da aski da wasu abubuwan na zahiri
zai iya zama Wajibi ko Mustahabbi gwargwadon
Maslaha ta Shari'a, kamar zuwa Kasar Kafiran
don Da'awa da kira zuwa ga Allah.
Shaikhul Islami ya ce: "Da a ce Musulmi yana
kasar abokan yaki, ko kasar kafirci ba abokan
yaki ba, to ba a umurce shi da saba wa Kafiran a
siffofi na zahiri ba, saboda abin da ke cikin haka
na samun cutarwa.

Kai, zai iya zama mustahabbi
ko wajibi a kan mutum wani lokacin ya yi tarayya
da kafiran a siffofinsu na zahiri (kamar Tufafi,
tara gashi ko aski), idan akwai maslaha ta Addini
a cikin hakan, na kiransu zuwa ga Addini, ko
leken asirinsu da kawo labari ga Musulmai, ko
kawar da wani cutarwa daga Musulmai da
makamancin haka na kyawawan Manufofi".

Saboda haka, matukar akwai maslaha ta Addini
to dacewa da kafirai a tufafinsu a cikin
garuruwansu wajibi ne ko mustahabbi.

In kuma
babu maslahar Addini hakan halal ne. Musamman
saboda yadda a yau ake zargin Musulmai Ahlus
Sunna da ta'addanci. Don haka Wajibi ne ga
wanda ya je kasashen Turai don yin da'awa ya
sanya tufafinsu".

Da wannan nake jan hankalin 'yan uwa Ahlus
Sunna, bai kamata muna kutsawa cikin abubuwan
da za su kara ta'assubanci da rabuwar kai a
tsakaninmu ba.

Sa'annan kuma yana da kyau mu
nisanci dukkan abin da zai zubar da haiba da
kwarjinin jagororin da'awar Sunna. Saboda yana
daga cikin manyan sabuba na
lalacewar al'umma idan ta wayi gari ba ta da
wasu jagorori a lamuranta da take ganin kimarsu
da kwarjininsu, a mayar da kowa bai wuce a ci
mutuncinsa da hakki ko ba hakki ba. Sai kuma in
wata matsala ta kunno kai mu fara lalubensu don
warware matsalar. Idan muka daraja jagororinmu
na da'awa da dukkan shugabanninmu sai mu
samu hadin kai da cigaban rayuwa.

Mu sani, kuskure ne mai girma abin da wasu
yan'uwa suke yi na hada hotunan malamai da
wasu cikin masu shirya fina-finai da da'awar
dukkaninsu daya ne! Har ma suke kiran wai a
daina magana a kan yan fim, tunda ga malamai
ma sun yi! Hakika wannan zalunci ne, domin
Allah ya bambanta su.

Kamar yadda na ga wani
dan'uwa mai kima; amma yana hada hotunan da
na wasu masu fina-finai a yayin da suke hade
mace da namiji, kuma har yake ganin ba su da
maraba
Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa kamar haka dadinkowa24.blogspot.com

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don ganin sabbin posting din Mu se ku duba saman website din akwai "Home" sai ku shiga, mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa nayau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com

Idan kana/kina da Labarin daku keson asanarwa da Duniya, ko Tambaya,Shawarwari,Hausa Novels, Nishadantarwa,Ilimantarwa,Ko Neman Sani akan ranakun dazamu cigaba dakawo muku Posting na Hausa Novels da Sauran su, zaku iya tuntubar ma'aikatan mu kuturo da Sunan Ku tareda Addreshin Ku tawannan Email din Officialdadinkowa24@gmail.com kyautane zamuyi muku komai don cigaban Al'ummar Hausa bama bukatar kudinka sai dai idan kaikayi niyyar Turowa don siyan Data Saboda acigaba dayin Posting a Kodayaushe batareda dakatawa ba, Website din Mu bashi da Alaka ta kusa ko tanesa da Wani/Wata Dan Siyasa/'Yar Siyasa afadin Duniya Burin mu shine musamu amincewar Al'umma aika da Gudunmawarka,Labari,Shawara da sauran su a Addreshin mu na email ✉💌📩 officialdadinkowa24@gmail.com  hanya me sauki ko kuma daga kasan Website din akwai inda akasa

Name...
Email...
Message...

Sai Ku turo mana mun gode

Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri

ALLAH yabar Zumunci Amin

Source By   ©Dr. Aliyu
Muh'd Sani, Ibrahim Garba Ibn Nayaya

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: