Wednesday 20 December 2017

Karanta Yanzu Kaji: Macen Da Ke Da Wuyar Samu A DUNIYA- Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

Tura Wannan Zuwa

Sheikh Aminu Ibrahim
Daurawa Ya kamata mu
sani cewa mace daya ce
a duniya take da wuyar
samu, amma idan ka
samu irinta, kada ka
kuskura ka rabu da ita.

Ya halatta ka auri mace
fiye da daya, amma Ka
sani, mace daya ce kawai,
take yin tasiri a rayuwa,
wacce ranka kullum zai
kasance a kanta.

Babbar tambaya a nan ita
ce, wacece wannan
dayar? Ita ce wadda duk
da namiji yake muradin
samu a rayuwarsa, ita ce
wacce ke koyi da rayuwar
shugabar matan duniya
kuma diya ga Rasulallahi
(SAW), wato Nana Fatima
(Allah Ya kara mata
yarda).

Haka kuma ita ce wacce
kowace mace take fata ta
zama. Ga siffofinta guda
goma, Kamar haka:

1. Matar da ta yarda ita
mace ce, don haka ta
tanadi duk abin da ake
bukata a wajen mace.

2. Mace mai hikima da
azanci, wacce ta karanci
mijinta da kyau, kuma
take kauce wa duk abin
da zai haddasa matsala a
tsakaninsu.

3. Mace mai taushin hali
da nutsuwa, wacce miji
yake jin natsuwa idan
yana tare da ita.

4. Mace da kudi bai dame
ta ba, ita mijinta kawai
take so, ko da akwai ko
babu.

5. Mace mai hakuri da
juriya, babu gunaguni,
babu mita, da kai kara ga
iyaye ko kawaye.

6. Macen da ta dauki
kanta likita, mijinta mara
lafiya, domin ya sami
kulawa, ta
musamman da riritawa.

7. Mace mai saurin
daukar ishara, tana gane
shiru da magana, da motsi
da yanayin shigowa da
fita, samu da rashi da
kuma yanayin da ake ciki
a duniya ko a gari.

8. Mace mai sakakkiyar
zuciya, mara kulli da
ramuwa.

9. Mace mai karawa miji
kuzari da karfin hali, a kan
kyawawan manufofinsa.

10. Mace mai rikon
amanar aure, da soyayya
ga mijinta kawai.

Shafin komai da ruwanka, Dadinkowa24 munayin aiki Tukuru don jin dadin ku

Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa kamar haka dadinkowa24.blogspot.com

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin  website din akwai "Home" sai ku shiga, mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa nayau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com

Idan kana/kina da Labarin daku keson asanarwa da Duniya, ko Tambaya,Shawarwari,Hausa Novels, Nishadantarwa,Ilimantarwa,Ko Neman Sani akan ranakun dazamu cigaba dakawo muku Posting na Hausa Novels da Sauran su, zaku iya tuntubar ma'aikatan mu kuturo da Sunan Ku tareda Addreshin Ku tawannan Email din Officialdadinkowa24@gmail.com kyautane zamuyi muku komai don cigaban Al'ummar Hausa bama bukatar kudinka sai dai idan kaikayi niyyar Turowa don siyan Data Saboda acigaba dayin Posting a Kodayaushe batareda dakatawa ba, Website din Mu bashi da Alaka ta kusa ko tanesa da Wani/Wata Dan Siyasa/'Yar Siyasa afadin Duniya Burin mu shine musamu amincewar Al'umma aika da Gudunmawarka,Labari,Shawara da sauran su a Addreshin mu na email ✉💌📩 officialdadinkowa24@gmail.com

Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri

ALLAH yabar Zumunci Amin

Source By ©Hausa7

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: