Thursday 22 February 2018

KARANTA KAJI: SHIN DA GASKE YUSUF BUHARI YA RASU ???

Tura Wannan Zuwa

Fadar shugaban Najeriya ta karyata labarin da ke cewa dan shugaban kasar Yusuf Buhari ya rasu.

“Yusuf Buhari yana samun sauki a asibitin da yake jinya a kasar Jamus kuma likitoci suna sake duba kansa da ya bugu da kuma kafarsa,” in ji mai taimakawa Shugaba Muhammadu Buhari kan shafukan zumunta, Malam Bashir Ahmad, a hirarsa da BBC.

Wasu shafukan intanet ne suka wallafa labarin da ke cewa dan gidan shugaban kasar ya rasu a ranar Talata da yamma.

Sai dai Malam Bashir ya ce labarin ba shi da kanshin gaskiya, yana mai cewa “ko jiya [Talata] na yi magana da ‘yar uwarsa da ke jinyarsa a asibitin Jamus kuma ta shaida min cewa yana samun sauki sosai.”

Sai dai tun bayan da aka tafi da shi Jamus ba a sake jin wani abu na labarin halin da yake ciki ba daga bakunan wadanda ke da kusanci da fadar shugaban, ko da kuwa a kafafen sada zumunta ne.

Kakakin na shugaban kasa bai fadi ranar da Yusuf Buhari zai koma Najeriya ba.

A farkon watan Janairu ne aka sallami dan Shugaban kasar daga wani asibitin Abuja bayan hadarin da ya yi a watan Disamba.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban kasar shawara kan harkokin watsa labarai Garba Shehu ya fitar, ta ce lamarin ya faru ne a unguwar Gwarimpa da ke birnin da daren ranar Kirstimeti.

A cewar Garba Shehu, “Ya karye a kafa sannan ya ji rauni a kansa sakamakon hatsarin. Kazalika an yi masa tiyata a wani asibiti da ke Abuja amma yanzu yana samun sauki”.

‘Ya’yan masu hannu da shuni kan yi wasan tseren babura akai-akai a wani yanki na kwaryar birnin Abuja, lamarin da ake gani na cike da hatsari.

A shekarun baya, hukumar birnin tarayyar ta haramta yin irin wannan tsere bayan wasu rahotanni da aka samu na tukin ganganci da masu tseren ke yi.

Source by ©Arewaplaza

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: