Friday 16 March 2018

Karanta Kaji Dalili: Saudiya za ta kera makamin nukiliya saboda Kasar Iran

Tura Wannan Zuwa

Saudiyya ta yi gargadin cewa ita ma za ta kera makamin nukiliya idan har abokiyar hamayyarta Iran ta mallaki makamin.

Yarima mai jiran gado Mohammad bin Salman ya shaidawa kafar yada labarai ta CBS cewa kasarsa ba ta son mallakar makaman nukiliya.

"Amma babu tantama, idan har Iran ta mallaki makamin nukiliya, za mu kera namu ba da dade wa ba," a cewarsa.

Sannan a cikin tattaunawar da aka yi da shi, Yariman ya kira Ayatollah Ali Khamenei a matsayin Hitler.

Saudiya da Iran sun dade suna hamayya da juna a yankin gabas ta tsakiya.

Kuma sabanin kasashen biyu ya samo asali ne daga banbancin akidar addinin Musulunci.

Saudiya na bin tafarkin akidar Sunni, yayin da kuma Iran ke bin akidar Shi'a.

Haka kuma bangarorin biyu sun dade suna hannun riga da juna a yake-yaken da ake yi a gabas ta tsakiya musamman rikicin Syria da Yemen.

Barazanar Saudiyar a yanzu na nuna fargabar yiyuwar shiga yakin makaman nukiliya a yankin na gabas ta tsakiya.

Iran dai ta yi alkawalin takaita ayyukanta na mallakar makamin nukiliya karkashin yarjejeniyar 2015 da ta amince tsakaninta da manyan kasashen duniya zamanin mulkin Shugaban Amurka Barack Obama.
Sai dai kuma shugaba mai ci Donald Trump ya yi barazanar janye wa daga yarjejeniyar.

Tun a 2015 da aka kulla yarjejeniyar, Saudiya ta kalubalanci matakin.
Saudiya ta fito ta yi gargadin cewa, bawa Iran damar ci gaba da shirinta na nukiliya, dama ce ga wasu kasashe a yankin su fara kera nasu makaman na kare dangi.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku
Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Muryarhausa24.com don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum

An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com
Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Muryarhausa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki
daya Amin Summa Amin.

Source by©Bbc Hausa

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: