Monday 19 March 2018

Karanta Kaji: Rawar Fatima Ganduje ta birge ni da ta gayyace ni tare za mu cashe - Saratu Gidado (Daso)

Tura Wannan Zuwa

A yayin da mutane maza da mata da kuma da musamman ma malaman addinin musulunci da dama suka yi ta suka tare da Allah-wadai da irin yadda diyar gwamnan Kano, Fatima Abdullahi Umar Ganduje ta zazzagar da zallar farin cikin ta a lokacin bikin ta, ita kuwa jaruma Daso ta yi tsokaci kan lamarin.

Kamar dai yadda muka samu, jarumar ta shirin fina-finan Hausa watau Saratu Gidado da aka fi sani da sunan Daso ta bayyana cewa ita amaryar birge ta ma tayi domin kuwa ta nuna farin cikin ta a fili.

Tauraruwar fina-finan Hajiya Saratu Gidado haka zalika ta kara da cewa ita da ma ta gayyace ta to da duk wannan rawar da ita za'a yi ta domin kuwa ita irin wannan ranar sau daya take zo wa mutum a rayuwar sa.

Mai karatu dai zai iya tuna cewa Shugaban hukumar nan ta tabbatar da da'a tare da dabbaka tarbiyya a jihar Kano ta Hisba watau Sheikh Malam Aminu Daurawa daga karshe ya yi tsokaci game da auren diyar Gwamnan jihar Fatima Abdullahi Ganduje da kuma angon ta Idris Ajimobi da ya gudana a jihar.

A cewar sa, a ranar Asabar jim kadan bayan kammala dauren auren ne ya tafi jihar Sokoto domin halartar bikin kaddamar da littafin Mansur Sokoto daga nan kuma ya tafi jihar Zamfara kafin kuma ya wuce Kaduna inda anan ma yayi wa'azi sai a jiya ma ya dawo.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku
Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Muryarhausa24.com don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum

An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com
Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Muryarhausa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki
daya Amin Summa Amin.

Source by©Hausa naija

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: