Tuesday 29 May 2018

Karanta Yanzu Kaji: Yau Ce Ranar Tunawa Da Zagayowar Mulkin Dimokradiya A Najeriya

Tura Wannan Zuwa


Ranar 29 ta watan Mayun Shekarar 1999 Najeriya ta koma mulkin dimokradiya daga mulkin soja kuma tun daga lokacin aka ayyana ranar a matsayin ranar Dimokradiya wadda kowace shekara ake tunawa da zagayowarta kamar yadda ake yi yau a duk fadin kasar.

A wani gefen kuma gwamnatin APC a karkashin shugabancin Muhammad Buhari ta cika shekaru uku cur tana mulkin kasar. Gwamnatin tasa tana samun yabo daga wasu ‘yan Najeriya dake ganin ta taka rawar gani, musamman wajen yaki da cin hanci da rashawa da fatattakar ‘yan kungiyar Boko Haram dake tada kayar baya a yankin arewa maso gabashin kasar.

Amma ‘yan babbar jam’iyyar adawa ta PDP suna ganin babu wani abun a zo a gani da gwamnatin APC din ta tsinana cikin shekaru ukun da tayi tana mulki.

To saidai gwamnan jihar Neja Alhaji Abubakar Sani Bello ya ce su aikin raya kasa suka sa agaba ba maganar jam’iyyar PDP ba.

Gwamnan na jahar Nija yace ba maganar wata jam’iyya ko ma PDP, jam’iyyar da ya ce ta mulki Najeriya na tsawon shekaru 16.

Ya ce shi kansa ya yi PDP din. Sun san irin dukiyar da aka samu a can baya da irin almubazarancin da aka yi. Gwamnan ya ce da gwamnatin shugaba Buhari bata zo ba da watakila ma yanzu babu kasar saboda irin mawuyacin halin da kasar zata shiga.

Duk da furucin gwamnan, jam’iyyar ta PDP ta ce tana ganin haske a gaba dangane da babban zaben badi kamar yadda shugaban jam’iyyar na jihar Neja Barrister Tanko Beji ya fada. Y ace sun yi na’am da irin goyon bayan da jama’a ke basu. Yanzu dai ana jiran lokaci ne kawai.

A Najeriya ranar 29 Watan Mayu ne ake bukuwan ranar zagayowar komawa ga mulkin Dimokradiya a kasar.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin aiki Tukuru don jin dadin ku Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin website din akwai "Home" sai ku shiga,

mungode

Muryarhausa24.com Zata Kasance Babbar Kafar Yada Labarai aduk fadin Duniya domin Bunkasa Harshen Hausa, domin Zafafan Labarai ziyarci www.muryarhausa24.com

Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com

Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin Muryarhausa24.com aduk inda kuke a fadin Duniya farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24.com shine ta fito da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi
me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@
gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki daya Amin

Source by ©VOA HAUSA
TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user