Thursday 8 November 2018

KARANTA KADAN DAGA CIKIN ALAMOMIN GANE MASOYIYA TA GASKIYA

Tura Wannan Zuwa
A lokacin da kake ‘ko’karin gano matsayinka a zuciyar budurwarka shin tana son ka ko akasin haka da akwai bu’katar ka nazarci wasu abubuwa wad’anda wasu sun kasance waiwaye ne wasu kuma suna kan faruwa.




FARKON HA’DUWAR KU.

YANAYINTA DA KUMA HALAYYARTA.

FARKON HA’DUWAR KU

A yayin gabatar da soyayyarka gare ta ka yi amfani da salo ne mai karsashi wato sai da ka gama jan hankalinta da ra’ayinta a kan ka sannan ka bayyana a gareta da lamari na soyayya?

Furta kalaman amince wa na soyayya ga wanda suke so abu ne da mata suke jin kunyar furta wa a karon farko ga samarin na su, sai dai duk da haka zata ke nuna maka alamun tana son ka kuma zata ke nuna maka wasu alamomi da suke nuni da SO.

Salon da kake bi wajen gudanar da soyayyar ta ku shi ne sikelin auna ci-gaba ko ci-bayan soyayyar ta ku, misali a lokacin da kuke tsaka da soyayya sai ta samu wani da ya fika iya kalaman soyayya da barkwanci da rashin yawan mita da dai duk wani salo mai burge wa to babu shakka ko kafi ‘karuna dukiya zai iya d’auke hankalinta da ga kan ka, sai dai ta tsaya da kai dan kud’inka.

A saboda haka akwai bu’katar ka kasance mai sabunta salonka na soyayya tun daga kan kalamai da yanayin yadda kake bata kulawa da sauran su lokaci bayan lokaci.

A dukkan lokacin da ka bu’kaci mace ta baka amsar amince wa tana son ka sai ka ga ta yi murmushi ko ta kasa furta hakan a karo na farko to hakan yana daga cikin alamu na SO domin kuwa wanda ake so ake jin kunya.

Karda ka damu da sai ta furta maka kalmar tana son ka kai dai lura da wad’annan abubuwa kamar haka;

Sau nawa kake kira kafin ta amsa?

Idan har da so zata amsa a kira na farko idan kuma bata amsa ba zata amsa a kira na biyu har ta baka uzurin da zaka gamsu na dalilin rashin amsa kiran, idan har bata amsa a kira na biyu ba sai ka bar kiranta haka idan har da so zata kira ka da zarar ta ga kiranka da ta rasa har ta baka uzurin kare kai.

Matu’kar tana son ka za ta kasance mai kar’bar shawarar da duk ka bata kuma za ta kasance mai son abun da kake so.

A duk lokacin da ka je wajen ta zance za ta fito cikin farin ciki kuma ba zata nuna ‘kosawa da jin firarka ba matukar ka iya zance har zuwa lokacin da za ku yi sallama.

Idan har ka saba kiran ta a waya matu’kar ta damu da kai idan ka kwana biyu baka kira ta ba to za ta kira ka ta ji ko lafiya, idan ma bata kira ba saboda wani dalili bayan ka kira za ta yi kalamai na nuna ta yi kewar ka.

Idan har tana son ka a kullum za ta ke ‘ko’karin yin abun da zai faranta ranka, za ta ke ‘ko’karin guje wa abun da zai sa ka yi fushi.

A lokacin da soyayyarku ta yi nisa zata iya bayyana maka wasu sirrikanta da suka shafe ta.

A lokacin da ka nuna ‘bacin ranka a kan wani abu da ta aikata da ba dai-dai ba, a yayin baka ha’kuri da shawo kan ka za ta iya zubar da hawaye.

Zata ke ‘ko’karin bayyana ka ga ‘kawaye da kuma ‘yan gidansu.

Zata ke ‘ko’karin turo maka da kalamai na soyayya.

Zata kasance mai tambaya a dangane da ‘yan uwa da kuma abokanka da ma dai duk wani da ta san kuna a tare.

Za ta ke damuwa da damuwarka.

Irin wad’annan abubuwa da sauran ire-iren su duk zai kasance ta na nuna maka su.

YANAYINTA DA KUMA HALAYYARTA.

Akwai bu’katar ka fahimci yaya yanayinta da kuma halayyarta suke,
Shin tana da jan aji ne da yawa?

Wanda hakan ka iya sawa ko tana son ka ba zata amince da kai a karon farko ba har ma za ta iya yin wasu abubuwa da zaka iya tinanin wula’kanci ta yi maka, amma da sannu matu’kar ka iya allonka za ka wanke.

Tana da kunya ne? ta yadda ba za ta iya sakin jiki da kai ba a karon farko kuma bayan tana son ka, idan ka yi ha’kuri da sannu soyayyarka za ta cire mata wannan kunyar da take ji a kan ka domin kuwa idan aka juri zuwa rafi da sannu tulu yake fashe wa.

Koda a ce bata da son kud’i farkon soyayyar ku sai ya kasance ka fara yi mata kyaututtuka to da sannu idan ka matsa da yi mata kyauta son abun hannunka zai rinjayi son da take yi maka na gaskiya, an dai kuma ce kyauta tana ‘kara soyayya, amma kuma komai ya yi yawa to zai kawo matsala.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: Tafarkin Tsira

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user