Tuesday 16 April 2019

KARANTA KAJI: DARASI GAME DA HARIN MASALLACIN KASAR NEW ZEALAND - Aliyu Imam Indabawa

Tura Wannan Zuwa
A wannan maqaala zanyi tsokaci ne bisa darasin daya kamata a tsinkaya game da harin 'yan uwa musulmi a kasar New Zealand, musamman garemu musulmi da kuma wadanda ke adawa musulunci.






Marubuci: Aliyu Imam Indabawa

Duk Musulmin dake da kaifin Kwakwalwa gami da karfin tadabburi zai dauki darasin rayuwa game da irin karamcin da musulunci ya samu a kasar New Zealand bayan harin da aka qaddamar.

A wancan lokaci mun ga yadda aka dinga gudanar da kiran sallah a sassan duniya, da kuma yadda Shugabannin kasar New Zealand suka nuna damuwarsu da tausayawarsu ga musulmi matuka, inda Prime Minister wannan qasa ta lazamci saka Hijabi na dan wani lokaci don girmamawa ga musulmi, Haka nan wannan mata munji yadda ta janyo hadisin Manzon Tsira S.A.W. idon duniya, mun ga yadda aka dinga watsa khudubar juma'a a gidajen TV a sassan duniya. Haka nan mun kalli yadda Gwamnatin wannan kasa ta bayar da damar karanta Al'qurani mai girma a majalisarta tare da girmama 'yan uwanmu Shahidai.

Har ila yau dai, mun ga yadda dubbun nan 'yan kasar wadanda ba musulmi ba sukai fitar dango domin zaman makoki ga musulmi, wannan kadai ya ishi ya taba zuciyar me imani cewa mutuntaka ba addini bace, wata kololuwar kyautatawa ce a wannan rayuwa.

KALUBALE GAREMU MUSULMI.

Kada kishin Addininmu ya hanamu tausayawa wadanda aka zalunta koda ba musulmi bane, wannan shine tubalin da aka gina addininmu akai, idan muka duba tarihin Shugabanmu S.A.W cike yake da tausayi da jin kan raunana ciki har da yahudu da nasara, wanda hakan ya janyo dubunnan su zuwa Musulunci.

Yau a sami kisan kiristoci a wannan kasa da yawanmu murna zasu yi. Musulmin da zai jajanta laifin shi zamu gani, tabbas wannan ba hanya ce mikakkiya ba, domin addini dan siyasa ne, kuma dan nasiha ne.


DARASI GA MASU ADAWA DA MUSULMI


Masu adawa da addinin Allah su sani cewa ba'a kauda gaskiya da zalunci, Sa'banin hujja.

Mai abun fada ai baya fada.

Wannan ta'addanci da kuka kaddamar wa musulmi bai rage su da komai ba sai Daukaka, mun sami labarin yadda daruruwa ke shiga musulunci, yayin da dubbai suka fara bincike a kanshi.

Allah ya daukaka Musulunci Amin.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslim (Garkuwar Musulmi) cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA, TUNATARWA ADDU'O"IN LITTAFIN HISNUL MUSLIM (GARKUWAR MUSULMI) CIKIN HARSHEN HAUSA,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode








TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user