Tuesday 16 July 2019

KARANTA RUKUNAN AZUMI

Tura Wannan Zuwa
Amma rukunan Azumi guda biyu ne:

1. Niyya:

Azumi ba ya yiwuwa idan babu niyya,

لِقَوْلِهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ: "إنما الأعمال بالنيات"  (رواه البخاري ومسلم)

“Dukkanin ayyuka basa yiwuwa sai da niyya.” (Bukhari da Muslim).

Lokacin Iftar


Da mutum zai dauki niyyar Azumin watan Ramadan a daren da ake zaton ganin wata ya kwanta bacci da niyyar idan an ga wata zai yi Azumi, idan kuwa ba a gani ba, zai ci gaba da cin abincinsa, sai aka ga wata yana bacci. Da gari ya waye, sai ya tashi bai ci abinci ba, bai yi abin da yake bata Azumi ba, sai aka gaya masa jiya yana bacci an ga wata, to wajibi ne ya kame bakinsa, kuma bayan Salla ya rama Azumi daya.

لِقَوْلِهِ عَمَّرُ ابْنِ يَاسِرٍ رَضِيَ الله عَنْهُ: "مَنْ صَامَ الْيَوْمَ الَّذِى يُشَكُّ فِيهِ فَقَدْ عَصَى أَبَا الْقَاسِمُ."

2. Kamewa ga barin ci da sha

Rukuni na biyu daga cikin rukunan Azumi shi ne kamewa ga barin duk wani abinci ko abin sha ko jima’i.

لِقَوْلِهِ تَعَالَى: "وَكُلُوا وَاشْرَبُوا حَتَّى يَتَبَيَّنَ لَكُمُ الْخَيْطِ اْلأَبْيَضِ مِنَ الْخَيْطِ اْلأَسْوَدِ مِنَ الْفَجْرِ ثُمَّ أَتِمُّوا الصِّيَامَ إِلَى اللَّيْلِ." (سورة البقرة: آية 187)

Kafin Shan Ruwa


Ma'ana:

“Ku ci ku sha har izuwa ku bambance tsakanin farin zare da bakin zare daga hasken alfijir, sannan ku cika Azumi izuwa dare.” (Suratul Bakara: aya ta 187).

MUKALOLI MASU ALAKA:

KARANTA A KAN WA AZUMIN RAMADAN YA WAJABA

KARANTA YAUSHE AKE YIN AZUMIN WATAN RAMADAN

KARANTA FALALAR AZUMIN RAMADAN

KARANTA SU WA AKA YARDA SU JINKIRTA YIN AZUMIN WATAN RAMADAN


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode









TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user