Wednesday 17 July 2019

NAFI KOWA FARIN CIKIN KORAR SUPER EAGLE A WASAN AFCON 2019 - DATTI ASSALAFY

Tura Wannan Zuwa
Naji dadi da aka koro kungiyar kwallon kafa ta kabilar Igbo ko inyamurai (Super Eagle) daga gasar cin kofin nahiyar afirka.


Super Eagle


Har ga Allah ban so su kawo zuwa wannan lokaci na Quarter final ba, ana diban makudan kudin 'yan Nigeria ana kashewa  'ya'yan Inyamurai akan wata shirme kwallo, wanda hakan babu abinda zai amfanawa Nigeria da 'yan Nigeria sai asara.

Masoya kwallon kafa ina tayaku murna sosai da aka koro kungiyar kwallon kafa ta inyamurai, abin mamaki mutanen da kake gani Ahlussunnah ne na gaske suma an shagaltar dasu wasan kallon kafa har ssunabayyana bacin ransu.


Ra'ayin Datti Assalafy


AN ZARGENI RASHIN KISHIN NIGERIA

Maganar da nayi jiya akan kwallon kafa, wasu sun zarge ni da cewa wai bana kishin Nigeria, har da kiran waya daga wajen abokan zumunci.

Hakika inda akwai wani alfano da talakan Nigeria, musamman 'yan uwana Musulmai suke samu a dalilin kwallon kafa tabbas da zanyi kishinta, kuma da zanyi fatan Nigeria taci nasara a kowani mataki.

Amma sai naga babu abinda harkan kwallo yake karawa a Nigeria face talauci da asara, turawa sun mana wayo suna samun makudan kudi akan harkan kwallo, wanda yau inda zaka shiga wani kauye mai nisan gaske zaka iya samun gidan kallon kwallo suna zuba kudi, kudin na tafiya asusun ajiyar kudaden yahudu da nasara.

Sai kaga mutum a kauyen kayau ya haddace sunayen 'yan kwallo, idan ka titsiye shi kyakkywan karatun Fatiha bai iya ba, a majalisun matasa sun dena tattaunawa akan abinda zai amfane su, ya kuma amfani al'ummar su, sai dai jayayya akan kwallo kawai.

Kallon kwallo ya haddasa gaba da kiyayya a tsakanin matasa, ya shagaltar da matasa akan mayar da hankali ga abinda zai amfane su, yana hana 'yan uwa musulmai Sallah akan lokaci cikin jam'i, har kisa anayi a kan kwallo, yara kanana suna zuwa gidajen kallon kwallo su hadu da miyagun mutane suna koya musu munanan dabi'u da laifuka da ta'addanci da iskanci.

Yanzu turawa sun jefa wadannan 'yan uwa matasa da suka shagala da harkan kallon kwallon kafa cikin mummunan laifi na sana'ar caca (9ja bet), wanda karshen 'dan caca rikakken barawo yake komawa, caca na hana mai yinta tabuka komai a rayuwa, abinda turawa suka koyawa matasan mu kenan.

Akwai lokacin da majalisar dattijai a Nigeria tayi yunkurin hana cacar 9ja bet amma ba su kai ga nasara ba, alherin Allah Ya kai ga tsohon gwamnan jihar Borno Kashim Shettima, domin shine gwamna na farko da na sani ya haramta cacar kwallo ta 9ja bet, ya musu koran kaji daga jihar Borno.

Don nayi adawa da harkan kwallo bai kamata  ace bani da kishin Nigeria ba, dangantani da rashin kishin Nigeria akan don nayi adawa da kwallo cin mutunci ne da kuma batanci da rainin hankali gareni wanda ba zan lamunta ba, rayuwata na Sadaukar akan kishin Nigeria da kuma zaman lafiyar Nigeria.

Yana daga cikin hanyoyin da yahudu da nasara sukace zasu yi amfani dashi wajen halakar da al'umma shine wasanni.

Ina rokon Allah Ya kara nakasa tasirin kwallon kafa a Kasarmu Nigeria.

Yaa Allah Ka cirewa 'yan uwa musulmi sha'awar kallon wasan kwallon kafa a cikin zukatansu Amin.

Allah Ya taimake
mu akan gaskiya.


MU KALOLI MASU ALAKA:

KARANTA ZAFAFAN SHAWARWARI 10 ZUWA GA SHUGABAN KASAR NIGERIA MUHAMMADU BUHARI

KARANTA LAIFIN DA SHUGABAN KASAR MISRAH MUHAMMAD MURSI YA AIKATA A IDON DUNIYA

KALLI YADDA SA'IN SA YA JAWO WATA TA CAKA MA WANTA WUKA YA MUTU HAR LAHIRA


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode






Source: Datti Assalafy

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user