Sunday 8 September 2019

KARANTA KAYATACCEN LABARIN WATA MATA DA KWARTAYE BIYU

Tura Wannan Zuwa
Akwai wani mutum, daya daga cikin askarawan wani Sarki. Ya kasance yana soyayya da wata mace 'yar talaka.

Wata Mata da Kwartaye Biyu


Daga littafin LABARAN DARE DUBU DA DAYA

Fassarar

Ibrahim Malumfashi

Danladi Haruna

Bukar Mada

Wata rana sai ya aiki wani yaronsa domin ya kai mata sako a gidanta, kamar yadda yakan yi daga lokaci zuwa lokaci. Yayin da yaron nan ya kai wa matar sako sai ta yi ta tsokanarsa da wasanni na jan ra'ayi, ta rungume shi cikin kirjinta. Ba ta gushe ba tana jan hankalinsa har ta takalo masa da sha'awa, ta jefa shi bisa shimfida, suka rungume juna.

Suna cikin aikata masha'a sai ga askar din nan, ubangidan yaro, ya zo yana kwankwasa kofa. Nan da nan matar ta boye shi a cikin wani dan karamin daki. Ta je ta bude wa masoyinta kofa, ya shigo yana rataye da takobi, ya zauna bisa shimfida. Matar ta zo ta rungume shi tana sumbata, har dai suka kwanta bisa shimfida suna rungumar juna. Suna cikin wannan hali sai ga mijin matar ya dawo yana kwankwasa kofa. Askar ya tambaye ta, "Wane ne?"

Ta amsa masa, "Mijina ne."

"To, ina dabara?" Askar ya tambaya.

Matar ta ce, "Ka zare takobinka, ka yi ta nuna ni da shi kana zage-zage, ranka a bace. Da zarar mijina ya shigo sai ka fice daga dakin kana huci, kada ka ce masa uffan."

Askar ya aikata kamar yadda matar ta umurce shi, ya zare takobi yana ta zage-zage. Ta tashi da sauri ta bude wa mijinta kofa. yayin da mijin ya shigo sai askar ya mayar da takobinsa cikin kube, ya fita yana huci, mijin ya bi shi da kallo, baki wangame, har ya fice. Daga nan sai ya juya ya tambayi matarsa, "Me ya faru?"

Matar ta ce, "Kai dai bari mai gida, Wallahi na gode wa Allah da ka dawo cikin lokaci, ba don haka ba da an yi kwababba." Mijin ya yi tsaye dai yana sauraron ta. Ita kuma sai ta ci gaba da cewa, "Ka sani ya kai mai gida, yau ka kubutar da saurayi daga kisa. Ina zaune bakin kofar daki ina kadi sai ga wani saurayi ya shigo gidan nan da gudu, yana haki kamar ransa zai fita. Ya fadi gabana yana cewa in yi masa rai, ga askar nan daga cikin askarawan Sarki ya biyo shi da takobi tsirara zai kashe shi. Ni kuma sai na ji tausayinsa, na ja shi da sauri na kulle cikin dan karamin dakin nan namu. Ina boye shi sai ga askar ya fado cikin dakin, kamar wanda aka bankado, da takobi tsirara, yana cewa in fito masa da saurayin da na boye. Na ce masa ni ban ga wani saurayi ba, ya tsaya yana ta zage-zage, yana cewa lalle sai na fito masa da shi. Muna cikin wannan jayayya sai ga ka ka fado. Wallahi Allah ya kyauta al'amurra da ka dawo da wuri."

Mai gida ya rike baki cikin mamaki, ya ce wa matarsa, "Ai wannan ba karamin allheri kika aikata ba, Wallahi Allah kadai zai biya ki ladan wannan taimako da kika yi." Ya shiga inda saurayi yake boye ya ce masa, "Fito ka tafi."

LABARAI MASU ALAKA:

KARANTA KAYATACCEN LABARIN ZAKI DA MUTUM

KARANTA KAYATACCEN LABARIN WATA MARAINIYA DA DAN SARKI

KARANTA KAYATACCEN LABARIN WANI AKU DA MATAR UBANGIDANSA

Saurayi ya fito yana makyarkyata don tsoro. Mai gida ya ce, "Saki ranka, kada ka ji tsoron komai domin babu abin da zai same ka." Da wannan makirci matar nan ta fitar da kanta, ba tare da mijinta ya zarge ta ba. Haka kuma sauran kwartayen biyu ba su san abin da ya faru ba bayan fitarsu.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode








TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user