Monday 7 November 2022

Alamomin Gane Soyayyar Gaskiya Da Gaskiya

Tura Wannan Zuwa

A lokuta da dama wasu masoyan suna tare da masu son su da gaskiya amma ba su sani ba.


Gane Soyayyar Gaskiya
Hoto: HD Wallpapers

MarubuciNura Nakowa


Rashin fahimtar alamomin da za su bayyana soyayyar gaskiya shi yake sa masoya su yi ta bilayi suna taraddadi a soyayyar su.


Ba a ƙulla alakar so da nufin ɓatanci ko baƙanta wa juna sai dai idan ba da manufar alkhairi aka zo ba. To wannan shi ne dalilin da yasa wasu masoyan (maza da mata) suke kokwanton ko wanda suke tare da shi da gaskiya ya zo kokuma akasin haka.


Ba dukkanin soyayya ce ake farawa da manufar aure ba amma kuma daga baya sai a ƙudurci aure kuma a yi auren. Wata soyayyar haka za a soma ta har a gamata ba ayi aure ba. To amma wannan ba yana nufin ba a so juna da gaske bane, a'a, da akwai wasu dalilai masu tarin yawa da suke hana soyayya ta kai ga yin aure.


Da akwai wasu alamomi guda goma sha biyar da na kawo su a cikin littafi na mai suna "Mene Ne Soyayya" waɗanda za su taimaka ƙwarai wajan gane soyayyar gaskiya da kuma irin dacewar da ka yi a soyayyar ka.


Ga kaɗan daga cikin su kamar haka:-


1. Za ka ga kuna samun dama da lokacin kasancewa a tare domin farantawa juna da kuma bayyanawa junanku abin da ke a cikin ran ku.


2. Idan bakwa tare zai zama tamkar kuna a tare ne. Alal misali; idan ba a gida ɗaya kuke ba ko kuma ba kwa kusa da juna kokuma ɗayanku ya yi tafiya zuwa wani garin, to zukatanku suna tare da juna ba sa rabuwa. Kuna kulawa da haƙƙoƙin junan ku tamkar kuna tare. Ba kwa aikata abin da ɗayan ku ba ya so koda kuwa a bayan idanunsa ne. Haka kuma za ka ga kuna kulawa da juna ta hanyar kiran waya da turawa juna saƙonnin soyayya ko kuma na wani sha'anin dabam.


3. Za ka ga saɓanin da ke shigowa tsakaninku ba mai tsanani ba ne, kuma idan aka samu rashin jituwa a tsakaninku cikin hikima da dabara kuke sasantawa.


Ragowar alamomin guda goma sha biyu suna ƙunshe a cikin littafin Mene Ne Soyayya wanda na yi muku bayani a baya. 


Kai dai ka nemi naka a kasuwa domin kada ka tsinci kanka a cikin chakwakiyar soyayyar da ba za ka iya warwarewa ba.


Guraren da za a iya samun littattafai na guda biyu "Sinadarin So" da "Mene Ne Soyayya" sun haɗar da....,


1. Arewa Radio 93.1 da ke lamba 64 a unguwar farm centre kusa da gidan kallo na Marhaba.


2. KASUWAR KURMI:- Abin Yabo Book Shop wajan Abu Huraira - 08036527328.


3. ƘOFAR FAMFO:- Shagon TJ Zarewa mai kayan wuta - 07039582763.


4. ZOO ROAD:- Bayan Hikima Multi Media wajan Salisu Maizare - 08175935495.


5. DAKATA:- Sunusi mai cajin waya bakin kasuwar dakata - 07066016221.


6. RIJIYAR LEMO:- Naziru Messi me kanti rijiyar lemo yammata gabas - 08066546638.


7. NA'IBAWA:- Megga Solution Internet Cafe dake jikin masallacin juma'a na uhud a na'ibawa 'yan lemo.


8. ƊORAYI:- Sutudiyon Habeeb Director dake gidan dakali saman benen gidan buredi - 09036686868.


9. BRIGADE ƘAURA GOJE:- Ras Communication - 08163972880.


A wannan lokacin ana sayar da kowanne akan kuɗi naira ₦300, idan kuma duka biyun za ka haɗa za a ba ka akan ₦500.


A ci-gaba da bibiyar mu a ranakun litininlaraba, da juma'a domin ganin abin da muka wallafa na soyayya.

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user