Thursday 28 March 2024

Abubuwa 28 Wadanda Ya kamata Ku San Su Game Da Ranar Alkiyama

Tura Wannan Zuwa

Allah ya ambaci sunayen ranar alƙiyama da sunaye mabambanta har guda ashirin da takwas. Za mu yi muku bayaninsu ɗaya bayan ɗaya da ma'anoninsu da kuma ayoyin da aka ambace su a cikin Alkur'ani.


JERIN SUNAYEN RANAR ALƘIYAMA A CIKIN QUR'ANI TARE DA MA'ANONINSU
Hoto: Awaz The Voice


Marubuci:- Imam Aliyu Indabawa


1- Ranar alƙiyama. An ambaci wannan sunan a wurare saba'in a Alkur'ani. Kamar faɗinsa maɗaukakin sarki

"  وَيَوْمَ الْقِيَامَةِ تَرَى الَّذِينَ كَذَبُوا عَلَى اللَّهِ وُجُوهُهُم
مُّسْوَدَّةٌ
Ma'anar ranar alƙiyama shi ne ranar tsayuwa. Kamar inda Allah ke cewa" 
يوم يقوم الناس لرب العالمين"


2. An ambace ta da Yaulmul Aakhir wato ranar ƙarshe kenan wacce ba wata rana bayanta. Kamar faɗinsa Allah cewa" إِنَّ الَّذِينَ آمَنُوا وَالَّذِينَ هَادُوا وَالصَّابِئُونَ وَالنَّصَارَى مَنْ آمَنَ بِاللَّهِ وَالْيَوْمِ الْآخِرِ وَعَمِلَ صَالِحًا فَلَا خَوْفٌ عَلَيْهِمْ وَلَا هُمْ يَحْزَنُونَ


3. An ambace ta 'Assaa'ah' kamar faɗinsa Allah cewa "
إِنَّ السَّاعَةَ آتِيَةٌ أَكَادُ أُخْفِيهَا لِتُجْزَىٰ كُلُّ نَفْسٍ بِمَا تَسْعَىٰ

Al'imam Alqurtabiy ya bayyana ma'anar Assa'ah da cewa "
أنّ الساعة تدلّ في اللغة على جزءٍ من الزمن دون تحديدٍ، وسُمِّيت القيامة بالساعة؛ إمّا من باب قُرب وقوعها، وإمّا تنبيهاً على ما فيها من أمورٍ عظيمةٍ، وقِيل لأنّها قد تأتي فجأةً في أيّ وقتٍ"

A harshen larabci kalmar saa'a na nufin wani yanki daga lokaci wanda ba a ƙayyade ba. An ambaci Alƙiyama da Assa'ah ne ko don kusancin faruwarta, ko don gargaɗi a kan manyan al'amuran da ke cikinta. An kuma ce ta kan zo kowanne lokaci wanda ba a yi zato ba.


4. An ambace ta ranar tashi. Kamar faɗinsa maɗaukakin sarki cewa "
ثُمَّ إِنَّكُمْ يَوْمَ الْقِيَامَةِ تُبْعَثُونَ


An ambace ta da haka ne saboda a cikinta ne ake raya matattu ake tashinsu daga kaburburansu.


5. An ambace ta ranar fitowa kamar faɗinsa ta'ala cewa"

يَوْمَ يَسْمَعُونَ الصَّيْحَةَ بِالْحَقِّ ۚ ذَٰلِكَ يَوْمُ الْخُرُوجِ


An ambace ta da hakan ne domin a ranar ne mutane ke fitowa daga kaburburansu zuwa tsayuwa.


6. An ambace ta ranar rarrabewa kamar faɗinsa Allah cewa "
إِنَّ يَوْمَ الْفَصْلِ مِيقَاتُهُمْ أَجْمَعِينَ


An ambace ta da hakan ne domin a ranar ne Allah ke rarrabewa tsakain halittu.


7. An ambace ta ranar buɗi. Kamar faɗinsa Allah cewa "
قُلْ يَوْمَ الْفَتْحِ لا يَنفَعُ الَّذِينَ كَفَرُوا إِيمَانُهُمْ وَلا هُمْ يُنظَرُونَ"


8. An ambace ta da ranar addini.

Faɗinsa cewa" مَالِكِ يَوْمِ الدِّينِ

Malamai suka ce abin da ake nufi da addini shi ne sakamako. A ranar ne Allah zai yi wa bayinsa sakamako a kan ayyukansu.


9. An ambace ta ranar ƙara saboda tsananin ƙarfinta. Faɗinsa Allah cewa " فَإِذَا جَاءَتِ الصَّاخَّةُ


10. An ambace ta da Attammah Alkubrah. Faɗinsa Allah cewa
فَإِذَا جَاءَتِ الطَّامَّةُ الْكُبْرَىٰ


Attammah a lugar larabci na nufin al'amarin da mutum ba zai iya da shi ba.


11. An ambace ta ranar hasara. Misali faɗinsa Allah cewa "
وَأَنذِرْهُمْ يَوْمَ الْحَسْرَةِ إِذْ قُضِيَ الْأَمْرُ وَهُمْ فِي غَفْلَةٍ وَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ


Hasara a lugar larabci na nufin nadama mai tsanani musamman ga 'yan wuta a kan ayyukansu.


12. An ambace ta Algaashiyah. Faɗinsa Allah "
هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ الْغَاشِيَةِ

Akwai saɓanin malaman tafsiri a kan ma'anar wannan kalma. Kuma karatu ne mai zaman kansa ga shi ban son na tsawaita.


13. An ambace ta ranar dawwama.

Fadinsa Allah"
ادْخُلُوهَا بِسَلَامٍ ۖ ذَٰلِكَ يَوْمُ الْخُلُودِ


Rana ce da 'yan aljanna ke dawwama a cikinta.


A taƙaice don kar na tsawaita ga ragowar sunayen da aka ambaci ranar alƙiyama da su a Alkur'ani.

14. يوم الحساب
15. الواقعة
16. يوم الآزفة
17.  يوم الجمع
18. الحاقة
19. القارعة.
20 يوم التلاق
21. يوم التناد
22. يوم التغابن
23. يوم الوعيد
24. اليوم العسير
25. اليوم المشهود
26. يوم عبوس قمطرير
27. النباء العظيم
28. الجاثية


Kowane suna yana buƙatar sharhi amma lokaci bai ba da haɗin kai ba.


Hikimar yawaitar sunayen alƙiyama shi ne kowanne suna yana bayyana wata siffa tsayayyiya. Hakan zai ƙara tabbatar da imani a zukata. Rayuka su zamanto shiryayyu saboda ranar alƙiyama.


Allah ka ba mu dacewa a gobe alƙiyama Amin.

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user