Showing posts sorted by relevance for query Auwal Ilyas Adam. Sort by date Show all posts
Showing posts sorted by relevance for query Auwal Ilyas Adam. Sort by date Show all posts

Friday, 27 September 2024

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (2)

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (2)

Ya juyo ya soma tafiya sannan ya waigo ya ce, "Wallahi ba domin kada ka ce na matsa maka ba da na ƙara maka wani saƙon. Muhimmi ne kwarai na mance da shi. Jakada ya ce, "to matso ka faɗa min!" Suka sake rankayawa yana ta faɗa masa saƙo. Haka suka yi ta yi har kafin su ankara sai ga shi sun isa garin da Laila take.


Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Layla
Hoto: Wikimedia Commons

Marubuci:- Auwal Ilyas Adam


Jakada ya yi mamakin irin wannan soyayya, sannan ya ce da Majnun, "Babu buƙatar kai wa Laila saƙo gare ni domin kuwa ga shi mun zo garin da take." Da jin haka Majnun ya cika da farin ciki da murna. Ya faɗi sumamme don tsananin farin ciki.


Bayan ya farfaɗo Jakada ya ce masa, “Ba na so a gan ka, domin jama’a na iya kama ka su yi maka wulaƙanci kafin ka ga Laila. Ga wani kango can ka shiga ka zauna a ciki ka huta domin ka yi tafiya mai yawa. Zan isar da saƙonka ga Laila yanzun nan.”


Majnun ya yarda da shawarar Jakada ya shiga kangon nan ya zauna zuciyarsa na harbawa kamar ta tsage. Sakamakon tafiyar da ya sha duk ya yi futu-futu. Tufafinsa sun yi jawur da ƙura, gashin kansa duk ya kukkulle, ga ƙafafunsa sun yi fato-fato da ƙura da faso da kaushi. Ga shi nan dai yarbajila da shi. Duk da haka, da ya tuna cewar yana garin da Laila ta ke gaba ɗaya sai ya ji ransa ya yi fari fat. Ya cika da murna da farin ciki, zuciyarsa ta cika da bege ya riƙa rera waƙa yana cewa:


Na aika saƙona wajen masoyiya.


Zuciyata da rayukana gaba ɗaya.


Na miƙa su dukansu wajenki gimbiya.


Ke ce tawa haƙiƙa na faɗi gaskiya.


Na sallama miki kaina lahira da duniya.


Daga nan sai gajiya ta kama shi, ya ji yana so ya kwanta. To amma sai ya riƙa tunanin shin a wanne ɓangare Laila take? Domin ba ya so ya kwanta inda ƙafarsa za ta riƙa kallon jihar da take domin a wajensa hakan cin amanar ƙauna ne. Zai iya shurinta bai sani ba. Ya tsaya yana tunani, shin tana gabas ne ko yamma ko kudu ko kuwa arewa? Duk inda ya sa kansa sai ya tuna ƙila a wannan ɓangaren take, sai ya yi maza ya sake waje.


Daga baya dai sai ya samo igiya ya ɗaura a ƙafarsa ya samu gini ya ɗaura ƙafar, ya zamana yana reto kamar jemage. A wannan yanayi kuma bai fasa rera mata waƙa ba yana cewa:


Hajjina da Umarata na wajenki.


Makka ta da Madina na su ne ganinki.


Baitil Mukdis a wurina murmushinki.


Arzikina duk ni dai na ga dariyarki.


Na sallama kaina gaba wurinki.


Ƙishir ruwa na damunsa amma babu ruwa a kurkusa, haka ya haƙura wutar bege na hura shi, tana ƙone masa sassan jiki da zuciya.


Jakada ya yi sallama ƙofar gidansu Laila ta fito, ya ce mata, "Na yi ƙoƙari da gaske domin na yi miki magana, game da masoyinki Majnun wanda ban taɓa ganin tamkarsa ba a fagen so." Ya kwashe labarin duk yadda suka yi ya faɗa mata. Sannan ya ƙara da cewa, "Yanzu haka na bar shi a bayan gari domin gudun kada a wulaƙanta shi idan jama'a suka gan shi." Da Laila ta ji haka sai tausayinsa ya kama ta. Ta tafi wajen uwar goyonta ta ce mata, "Me yake faruwa ga mutumin da ya yi tafiyar mil ɗari da ashirin a ƙasa ba tare da ya huta ba?"


Tsohuwa ta ce, "Wannan mutumin ba zai rayu ba mutuwa zai yi." Laila na jin haka sai ta ji ta shiga damuwa, ta sake ce mata, "babu wani magani?" 


"Magani ɗaya ne a sanina. Dole ya sha ruwan saman da aka ajiye shi aƙalla shekara ɗaya, kuma dole ruwan ya zamana maciji ya sha daga gare shi. Sannan ya ɗaura igiya a ƙafarsa ya zamana kansa na kallon ƙasa zuwa wani lokaci. Idan ya aikata hakan wataƙila zai tsira da ransa."


Da ta ji haka sai ta yi tagumi tana cewa, "Wannan magani akwai wahalar samu, kai ba ma zai yiwu ba." Ta ɗaga hannu sama tana roƙon Allah ta ce, "Ya Allah mai ƙulla soyayya, mai bayarwa mai hanawa ka taimaki Qays Majnun ya samu wannan magani." Ta shafa sannan ta yi ajiyar zuciya ta ce, "Soyayya ba ta da magani sai ita kanta."


Allah da ikonsa, Majnun na rataye da ƙafarsa a sama ga ƙishirwa na addabarsa sai ya kwance igiyar ya tafi neman ruwa. Bai samu ruwa ba sai wani tsohon kasko a wani lungu. Ya tarar da wani zabgegen maciji na shan ruwan. Ya kore shi sannan ya kafa kai ya shanye ruwan gaba ɗaya. Ya samu waje ya zauna yana waƙe-waƙensa.


Da gari ya waye Laila ta shirya abinci mai rai da lafiya ta kirawo kuyanga a ɓoye ta faɗa mata komai sannan ta nemi ta kai wa Majnun inda yake a bayan gari. Kuma ta ba ta saƙon a faɗa masa cewar ita ma tana nan tana ƙaunarsa kuma tana son ganinsa, amma da zarar ta samu dama za ta zo ta gan shi. Yayin da Kuyanga ta je wajen sai ta tarar da mutane biyu. Ɗaya ya haɗa kai da gwiwa kuma duk ya rame ga kansa nan duguzunzum, ɗayan kuma mai kiɓa jawur da shi, sai dai ya manyanta. Kuyangar ta dube su duka biyun ta ga babu wanda ya cancanci Laila ta so shi.


Ita kanta ma ta ji duk ba su kwanta mata a rai ba, balle kuma Laila. Duk da haka domin cika umarni sai ta ce, "a cikinku wane ne Majnun?" Mai kiɓar ne kaɗai ya ji sai ya taso wajenta ya ce, "Me ya faru?"


Sai ta nuna kwandon abinci ta ce, "cewa aka yi na kawo masa wannan daga Laila." Nan da nan ya karɓe abincin yana cewa "Ni ne Majnun." Ta faɗa masa saƙon Laila ya yi mata ɗan wasa haka sannan ya sa abinci a gaba ya cinye. Ya ragewa Majnun ɗan kaɗan.


Daga wannan rana kullum sai ta kawo masa abinci da saƙon baka, shi kuma sai ya cinye ya rage kaɗan domin Majnun. Kullum Laila kan tambayi Kuyanga, "Me ya ce ki faɗa min?" Sai Kuyanga ta ce, "Wai ya gode madalla da abinci."


Laila ta shiga kokwanto anya kuwa Majnun ɗinta ne? Bayan kwana uku dai da ta gaji sai ta ce da Kuyanga, "Yaya kika ga kamannin Majnun din?" Kuyanga ta ce, "Wani mai ƙiiba yana da saje da ƙasumba...ya manyanta..."


Farat Laila ta ce, "Wallahi ba shi ba ne, wannan Jakada ne wanda ya kawo min saƙonsa. Majnun ba tsoho ba ne kuma ba shi da ƙiba." Ta dubi Kuyanga ta ce, "Su nawa ne a wurin?" Kuyanga ta ce, "Su biyu ne." Laila ta yi ajiyar zuciya ta ce, "to yau ba za a kai abinci ba, amma zan sa ki musu wata jarrabawa domin mu gane Majnun na gaskiya." 


Ta ba ta wuƙa ta faɗa mata abin da za ta yi da ita.


Kuyanga ta tafi wajensu Majnun, ta tarar da Jakada na tsaye yana jiranta. Tana zuwa ya soma yi mata sannu da zuwa. Ya miƙa hannu da nufin ya karɓi gara, maimako haka sai ya ga ta fito da wata sharɓeɓiyar wuka. Ta ce, "Laila ba ta da lafiya, ana buƙatar jinin masoyinta kwalba ɗaya wanda da shi za a haɗa maganin. Shi ya sa na zo wajenka na ɗiba."


Yana ganin haka sai jikinsa ya kama rawa ya ce, "To ni dai ba masoyinta ba ne, kuma ba ni ne Majnun ba, gashi can a zaune." Ta wuce zuwa wajen Majnun ta faɗa masa kamar yadda ta faɗa wa Jakada. Yana jin haka ya karɓi wuƙar da hanzari, ya sumbace ta sannan ya ce, "Na gode wa Allah da ya ƙaddara cewa jinina ne zai warkar da ciwon masoyiyata." 


Ya darzaza wuƙar a hannunsa, maimakon jini ya zubo sai wajen kurum ya yi farat fat, alamar babu jini. Ya sake keta wani wajen, nan ma babu jinin saboda bai ci abinci ba ballantana a samu abin da ake buƙata. Da ya ga haka sai ya soka wuƙar a hammatarsa inda babbar jijiyar jini take, nan jinin ya riƙa ƙwarara. Ya tara ya miƙawa kuyangar wadda tuni tsoro da mamaki sun hana ta motsi. Yayin da ta koma gida ta shaida wa Laila irin abin mamakin da ta gani wajen Majnun, sai Laila ta yi ta kuka tana tausaya masa.


A cikin gari kuwa, labarin Majnun ya cika gari, sai aka samu wasu shaƙiyan matasa suka ɗauko kulake suka nufi inda yake. Tun daga nesa da Jakada ya hango su sai ya hau taguwarsa ya sulale ya bar Majnun yana waƙe-waƙensa yadda ya saba. Matasan na zuwa suka hau bugunsa suna shuri da naushi da yakushi. Suka ɗaure shi da igiya sannan suka tsaya daga nesa suna jifarsa. Da Laila ta ji labari sai ta sheƙo da gudu ta zo ta kare shi daga bugun mutane, ta riƙa zaginsu tana korarsu. Shi kuwa duk da yana ɗaure ga bugun da ya sha amma sai ya ji ransa ya yi fari fat da ganin abar begensa ya riƙa ambaton sunanta yana cewa:


Laila, Laila, Laila tawa ce.


Domin a kanki ne na haukace.


Wasu na kallona wai na karkace.


To amma fa yau na samu dace.


Da ganin haskenki ya masoyiya.


Iyayen Laila suka turo aka tafi da ita gida tana kuka. Da suka ga lamarin ya wuce saninsu sai suka yi shirin yin balaguro na wani lokacin domin a tsammaninsu idan suka tafi suka jima Majnun zai gaji da nemanta har ya saduda ya haƙura.


Suka shirya kaya suka tafi wani gari da ba su ambata ba, gudun kada ya ji ya bi su can. To amma kafin su tashi Laila ta rubuta takarda a ɓoye ta ba wa kuyangarta ta kai wa Majnun. Ya buɗe ya karanta cewar "Masoyina, bulaguro za mu yi wani gari mai nisa, haɗuwar mu za ta yi wuya anan. Idan za ka iya mu haɗu a zangon farko cikin sahara.".


Yana gama karantawa ya ce da kuyangar, "Ki gaishe ta da kyau da kyau, kuma ki faɗa mata cewar ina nan tafe."


DUBA WANNAN: Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (3)


Lokacin da su Laila suka sauka a zangon farko ta tafi ita da kuyangarta zuwa inda ta ce masa ya je za ta same shi.


A tsammaninta bai isa ya zo wurin ba a wannan lokacin..........


Za mu ci-gaba Insha Allah.

Friday, 20 September 2024

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (1)

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (1)

Wani saurayi mai suna Qays ibn Mulawwah ɗan ƙabilar Banu Amar. Qays ya kasance mai fasaha da basira a makarantarsu, sai dai ya kamu da soyayyar Laila bint Mahdi Ibn Sa’ad an fi kiran ta da Laila Amiriya, a hankali ya riƙa nuna mata soyayya ta hanyar kulawa da sauran alamu.


Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila
Hoto: Eejjbair Medium


Marubuci:- Auwal Ilyas Adam


Duk lokacin da ta makara zuwa makaranta sai hankalinsa ya tashi ya rasa sukuni, gabaɗaya sai ya zuba wa ƙofa ido ba ya mayar da hankali ga karatunsa. Wata rana da zuciyarsa ta cika da bege, ya ji ƙirjinsa kamar ya fashe, bai san lokacin da ya riƙa rubuta sunan Laila a takardar rubutunsa ba maimakon abin da ake koya musu. Ɗalibai da suka ga haka sai suka haƙiƙance lallai ya yi nisa wajen ƙaunar ta. Da haka ita ma Laila ta soma ƙaunarsa ya zamana duk makarantar an san su a matsayin masoya.


Shi Qays kamar tun yana yaro ƙarami masu ilimin taurari suka bayyanawa mahaifinsa cewa zai kasance wanda rayuwarsa za ta faɗa cikin wahala da musiba. Suka ƙara da cewa idan ba a yi da gaske ba ma zai iya haukacewa. Tun daga wannan lokacin mahaifinsa ke samo masa laƙani da magunguna da addu’o'i. Yayin da ya data sai mahaifinsa ya ɗauke shi ya kai shi Dimashka karatu inda anan ne ya haɗu da Laila.


Ita Laila ta kasance ‘yar shugaban ƙabilar Sharwaris, wadda a da zamanin Jahiliyya ba sa ga maciji da ƙabilar su Qays. Laila da Qays suka zama tamkar jini ɗaya tsoka ɗaya, idan ɗaya bai ga ɗaya ba sai ya kama rashin lafiya, amma Qays abin na sa ya fi tsanani, domin kuwa har waƙoƙi yake rubutawa masoyiyarsa yana karanta su a ko’ina.


Ɗaya daga waƙoƙin da ya yi mata ita ce:


Na so ki ya mai kyau dan gaske.


Wane wata ko tauraro mai haske.


Kin shiga ruhina kin mammallake.


Idan babu ke to ni kuwa na hakkake.


Ba za ni rayu a duniyar nan ba.


A makaranta aka rinƙa gulmar su ana nuna Majnun duk inda ya wuce, sai ya kasance idan ka yi masa abu ka ce masa ya yi haƙuri don Laila, shikenan zancen ya wuce. Da ɗalibai suka gano lagonsa, suka riƙa ɗauke masa kayan rubutu suna cewa ya ba su domin darajar Laila. Ba musu sai ya ba su. Maubin (malamin) makarantar ya damu ƙwarai da irin wannan al’amari. Musamman da ya ga Qays wanda yanzu sunan ya ɓace ya koma Majnun Laila (Mahaukacin Laila) ya rubutawa iyayensu takarda yana faɗakar da su halin da ‘ya’yansu ke ciki. Iyayen Laila suka cire ta daga makarantar aka kirawo wani ƙwararren malami yana koya mata karatu a gida. Ciwon so ba shi da magani! Maimakon hakan ya yi magani sai ya daɗa rikita al’amari. Majnun ya daina karanta komai kullum sai kuka sai waƙa, duk abin da ya gani sai ya ga yana masa gizo da kamannin Laila. Nan da nan sai ya soma rera waƙar so gare ta.


Mahaifin Majnun ya zo takanas ya ɗauke shi zuwa wajen likitoci da ‘yan tsibbu da bokaye da sauran masu da’awar magani duk abin ya zama tamkar wutar kara ana yayyafa mata fetur.


Abokai da ‘yan uwa na kusa da na nesa suka zo domin tausasa zuciyar Majnun ya daina tunanin Laila amma duk a banza. Wani daga baffaninsa ya ce masa, “Wai kai Qays me ka gani a jikin Laila da ka nace mata haka? Ka zo mu je na nuna maka mata dubu waɗanda suka fit a kyau da kyan fasali da asali da mulki da dukiya da sarauta ka zaɓi wadda ta yi maka.” Majnun ya dube shi ya girgiza kai ya ce, “idanun Majnun Qays ba wanda suke so da gani tamkar Laila.” Ya ɗaga hannu sama ya ce, “Ya Allah! Na san ba ka yi kyakkyawa a duniyar nan tamkar Laila ba. Na tabbata ita tana daga asalin Hurul Aini da suka zo duniya shan iska. Ya Allah alƙawarinka ba ya tashi, na tabbata daga kan Laila ba za ka sake wata kyakkyawa ba. Ya Allah ka ba ni Laila!”


Wani daga ƙabilarsu ya ba mahaifin Majnun shawarar ya ɗauki Majnun zuwa Makka ya yi roƙo a ka’aba kan Allah ya ɗauke masa son Laila a zuciyarsa. Amma saboda tsananin soyayya a yayin da suka je ɗakin ka’aba sai mahaifinsa ya ce masa: kama tufafin ka’aba ka roƙi Allah ya cire maka son Laila sai Majnun ya kama ya ce: “Allah na tuba gare ka daga dukkan laifi, amma ba zan tuba daga son da nake yi wa Laila ba . . . Ya ƙara da cewa, “Ko Luqman, babban malami masani na tabbata ba shi da maganin ciwon so…Idan ma yana da shi ina fata babu wanda ke tsakanina da Laila. Ya rera waɗannan baitoci:


A Makka na ce da shehin malami, Wai shin wace ke cutar da ni?


Shin laifi ta ke yi to a sanar da ni.


Shehi ya ce “ɗana bi a hankali, Azaba na nan zuwa can gare ta.".


Na yi farat na ce masa “A'a na yafe, Da azaba ta samu Laila ko a gefe, ba ni ƙauna, gara ta same ni a gefe. Da na daina sonta a barci ko farke, gara na mutu da ciwon ƙaunar ta. Sannan ya ce da murya mai raurawa, “Allah ka ba ni Laila!”


Yayin da iyayen Majnun suka ga haka kullum lamarin nasa ƙara lalacewa ya ke yi, sai suka ga babu mafita face su je su nemi auren Laila wurin iyayenta. Wannan shi ne mataki na ƙarshe da suke ganin zai magance matsalar ɗansu.


Suka tashi jakadu na musamman zuwa garin su Laila suka bayyana musu irin halin da ɗansu yake ciki game da soyayyar Laila. Sannan jakadun suka nemi aurenta dominsa. Iyayen Laila suka amsa da cewa, “mu a wajenmu abin da Majnun yake yi domin ‘yar mu wulaƙanci ne mai girma. Kuma duk da yake mun san cewa Laila tana da ra’ayinsa amma ba za mu iya aurar da ita gare shi ba. A dalilinsa mun cire ta daga makaranta, mu a wajenmu, mahaukaci ne kaɗai zai riƙa irin abin da Majnun ke yi.”


Da haka iyayen Majnun suka ji daɗi tunda su a tsammaninsu idan har ya daina shiririta za su amince su aura masa ita. Saboda haka suka shiga tausasarsa suna ba shi shawarar ya nutsu ya daina abubuwan da yake. Majnun ya amince da haka, amma da sharaɗin za a kai shi ya ga abar ƙaunarsa Laila.


Suka shirya suka tafi tare da wakilansa zuwa garin su Laila. Aka sauke su a wani babban gida sannan aka kawo musu abinci da abin sha. An ƙawata wajen da fitilu masu launi iri daban-daban. Sannan a kunna turaren wuta ko'ina sai ƙamshi ke tashi. An jera kasake masu yawa cike da abinci da fulawoyi masu ƙayatarwa. Zuciyar Majnun kuwa ta kasa nutsuwa, ji yake kamar ya yi tsuntsuwa ya tafi ga masoyiyarsa.


Bai iya jurewa ba sai ya miƙe a gaban waliyan Laila ya riƙa safa da marwa yana rera waɗannan baitoci:


Na yi nisan zango don na gane ki.


Ga shi na zo nan ina ta biɗar ki.


Ina kike ina kika shiga ne in gan ki.


Zuciyata tana ta jidali domin nemanki.


Ya ki taho abar begena don Allah nunan kanki.


Jimawa kaɗan sai ga karen da Laila ke zuwa da shi makaranta ya shigo gidan. Majnun sai ya ji ya kasa jurewa, ya zabura wajen karen nan ya rungume shi yana sumbatarsa yana cewa, "Na ga rabin Laila saura rabin. Ya karen nan mai baiwa maza je ka ingizo min Laila." 


Garin wutsulniyar da kare yake yi da ƙafafu ya ture farantan abincin, suka ɓata gaban rigar wani dattijo mai faɗa aji a dangin Laila. Shi kuwa gogan naka sai ya ɗauki wani tsiron fulawa ya maƙalawa karen a wuya yana ce masa, "Maza je ka kai wa Laila ka miƙa min gaisuwata gare ta." Duk jama'ar wurin suka yi tsit suna kallon ikon Allah.


Wakilan da suka rako shi suka rasa inda za su sa kansu domin kunya.


Wakilan Laila kuwa suka cika da fushi iyakar fushi. Wani daga cikinsu ya fusata ya ce wa Majnun, "Shin bautar kare ka zo ko kuwa maganar aure?"


Kaitsaye Majnun ya kalli mutumin ya ce, "Wannan karen a wurina ya fi mutum dubu daraja, domin a jikinsa ina ganin surar masoyiyata wadda ƙaunarta ke ɗamfare a zuciyata dare da rana." Duk wuri aka ɗauki salati. Jama'a suka riƙa zunɗensa suna cewa ya haukace. Dattijon nan da aka ɓatawa riga da abinci ya miƙe a fusace ya fice daga gidan. Duk jama'a ma suka watse.


Da wannan jama'a suka riƙa rantsewa cewa haukan nan dai bai rabu da shi ba, sai ma abin da ya yi gaba. Daga nan iyayen Laila suka fito kaitsaye suka ce ba za su aurar da 'yar su ga Majnun ba. 


To daga nan sai duk wani fatan samun nutsuwarsa ya zama sharon gayya, suka haƙiƙance ba za su iya magance masa matsalar ba, don haka suka sa masa albarka suka ƙyale shi bisa halinsa. Shi kuwa duk inda ya shiga lungu da saƙo sai ya riƙa cigiyar Laila ko sun san inda take da yadda zai sadu da ita. A haka har ya yi kiciɓis da wani Jakada mai aikin raba takardu. Ya tambaye shi labarin Laila. Jakada ya ce masa "Laila da iyayenta sun tashi daga garinsu sun koma wani gari mai nisa, daga nan garin zuwa can tafiyar mil dari da ashirin ne." Majnun ya shiga yi masa magiyar yana ba shi saƙo zuwa gare ta.


Jakada ya amince zai karɓi saƙon takarda kurum babu wani abu. Majnun ya zauna ya yi ta rubutun shafuka da yawa, har Jakada ya gaji ya ce masa, "Wacce irin wasiƙa ce haka?"


Majnun ya ce, "Wasiƙar soyayya ce ba ta da ƙarshe."


Jakada ya yi dariya da haka sannan ya ce, "To samu waje ka ɗiga aya ka ba ni na tafi." Majnun ya naɗe takardar ya ba shi. Sannan ya nemi ya yi masa rakiya kaɗan. Suna tafe Majnun na ba wa Jakada labarin abar ƙaunarsa Laila shi kuma yana ta mamaki. Sai da suka shafe mil goma Majnun na tafiya a ƙasa Jakada na bisa raƙumi. 


Za ku iya ganin takaitaccen labarin kaitsaye a bidiyon nan..

Jakada ya ce masa, "To ka koma haka, ka yi nisa ƙwarai da gidanku." Majnun ya juyo ya soma tafiya sannan ya juya ya ce da Jakada da babbar murya, "Ya kai ƙaunataccen abokina! Wallahi na yi mantuwar wani muhimmin saƙo da nake so na rubuta mata!" 


DUBA NA GABA ANAN: Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (2)


Jakada ya ce, "To gaskiya ba zan tsaya ba, sai dai ka faɗa min da baki na faɗa mata".


Za mu ci-gaba Insha Allah.

Friday, 1 November 2024

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (5)

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (5)

Tamkar mai hauka haka Laila ta koma bayan da ta yi duk abin da za ta iya don ganin masoyin nata a farke, idanuwan Laila tuni sun ƙanƙance saboda tsabar kukan da ta ke yi.


Labarin Soyayyar Majnun Da Laila
Hoto: Kekisruhan

Marubuci:- Auwal Ilyas Adam


Cikin wata murya wadda kunne ba zai iya tantancewa ba ta fara rera wasu baitoci kamar haka:


Wanzuwata da numfashi na na gan ka a damana.


In ka bar ni anan duniyar ga wane ne gatana?


Yaka taso zo, ni ganin ka shi ne fatana.


Tana kaiwa ƙarshen baitocin sai ta ƙwala masa kira da ƙarfin gaske "Majnun!"


Can kuma a mahaɗar nan wadda daga nan ne za ka yi shirin shiga Habasha, wato inda iyayen Laila suka yada zango kenan, bayan iyayenta sun gama shiryawa tsaf sai mahaifiyarta ta duba ba ta gan taba, nan da nan ta sanarwa da mahaifinta halin da ake ciki, neman duniyar nan sun yi a wannan mahaɗar wadda take tamkar wani ɗan ƙaramin gari ne amma ba Laila ba alamarta, hankalin iyayenta ya tashi, anan wasu suka ba wa iyayen shawara akan su ƙarasa cikin Habashan ko wataƙila ta bi ayarin wasu gungun fataken ne.


Hakan kuwa akai wato iyayen Lailar suka amince da hakan, isar su Habashan keda wuya ba su zame ko ina ba sai fadar sarkin, a matsayinsu na su ma masu ƙaramar sarauta a masarautarsu, yayinda iyayen Laila suka labartawa sarkin Habasha labarin ɓatan 'yarsu da ma cikakken labarin Laila da Majnun ɗin, sai sarki da muƙarrabansa suka cika da mamaki yayin da wasu da yawansu suka ringa kuka saboda tausayin waɗannan masoyan, sarki ya haɗa wata tawaga ta mahaya ɗari ya ce su nufi can nahiyar da aka baro Majnun ɗin ko wata ƙila za'a gan ta a can wajensa, kuma ya ce musu idan sun gan su to su taho dasu gabaɗayansu zuwa fadarsa.


Gwauron numfashin da ya ja ne ya sa Laila ta karkato da hankalinta zuwa gare shi, tabbas Majnun ɗinta ne yake numfasawa, sannu a hankali ya buɗe idanunsa waɗanda ba sa iya buɗewa gabaɗaya saboda tsabar wahalar da Majnun ɗin ya sha, Laila ta dube shi cikin shashsheƙar kuka haɗe da dariya ta ce, "Majnun ni ce Lailarka, gani a tare da kai na dawo Majnun... Ba zan iya rayuwa ba ba tare da Majnun ɗina ba..." 


Duk da halin da yake ciki hakan bai hana bayyanar wani tattausan murmushi ba akan kumatunsa, cikin sanyin jiki ya lalubo hannun Laila ya matse shi gam a hannunsa tamkar yana tsoron kada wani abin ya zo ya kuma raba shi da Lailarsa.


DUBA WANNAN: KARANTA CIKAKKEN LABARIN SOYAYYAR LAILA MAJNUN 


Wata rana Majnun ya zo ya wuce ta gaban mai sallah yana begen Laila bayan mai sallah ya gama sai ya yi sauri ya sha gaban Majnun don ya ji dalilin da ya sa ya tsallaka mashi sallah?

 

Majnun ya dubi mai sallah ya ce


"Yaushe ka gan ni"


Mai sallah ya ce "Lokacin da nake sallah".


Majnunin Laila ya ce "Wallahi ina cikin begen Laila har na wuce ban gan ka ba, kuma Wallahi da soyayyar ka ga Allah ta kai kwatankwacin yadda nake son Laila to na tabbatar kai ma ba za ka gan ni ba.".


Ina jin anan zan tsaya da ba ku wannan ƙayataccen labarin.


Ku ci-gaba da kasancewa da ni domin jin wasu daɗaɗan labaran.

Friday, 4 October 2024

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (3)

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (3)

A tsammanin ta bai isa ya zo wurin ba a wannan lokacin, domin su a abin hawa suke, shi kuwa a ƙasa yake. Tana zuwa ta same shi ya haɗa kai da gwiwa yana ta kiran sunanta, "Laila! Ya Laila!! Ya Laila!!!" Ta ƙaraso wurinsa tana mai cewa, "Ya Majnunun Soyayya ga Lailarka ta iso!!". Duwatsun kusa da na nesa suka ɗauki muryarta tana amo.


Labarin Soyayyar Majnun Da Laila
Hoto: Dynamite of emotions

Marubuci:- Auwal Ilyas Adam


Nan da nan ya zabura zuwa gare ta, yana mai cewa, "Shin da gaske ne Laila ke ce anan?" Ta amsa "Ni ce!" Ya miƙa mata hannu ta riƙe sai suka ji kururuwar mahaifanta suna nemanta domin a ci-gaba da tafiya. Ta juya da hanzari, ya ce, "Haba Laila kada ki tafi ki bar ni da begenki!" Ta ce, "Kar ka damu, idan na dawo za mu haɗu anan."


"Yaushe za ki dawo?" Ya tambaye ta. Ta ce, "Ban san lokacin ba, amma da zarar mun taho zan aika maka." Da haka ta tafi ta bar shi anan. Majnun ya ce a ransa, "idan ta dawo wa za ta aika ya faɗa min? A ina ɗan saƙon zai same ni? Kawai bari na zauna anan ɗin har sai ta dawo." Ya share wuri ya zauna ba shi da wani abinci sai ganyen bishiyar da ke wajen yana shan ruwan da ke ɓuɓɓugowa daga ƙarƙashin dutse. A kullum zancensa shi ne kiran sunan Laila da addu'ar ta dawo ta same shi. A haka har tsiron bishiya ya fito daga 'ya'yan itacen da yake jefarwa, ganyenta ya nannaɗe masa jiki ya zama tamkar bishiyar a jikinsa ta tsiro.


A can garin da su iyayen Laila suka je da ita kuwa, sai wani attajiri ya fito yana son ta da aure. Nan take ya ba wa iyayen raƙuma ɗari gami da wasu kyautuka masu yawa. Da Laila ta ga alamar lallai za a aurar da ita gare shi sai ciwo ya kama ta. Ta yi ta fama, iyayen suka yi nufin komawa gida domin magani alabarshi idan ta warware sai a yi auren. A hanyar su ta dawowa suka sauka a wannan zangon. Duk da tana fama da jinya Laila ta taso zuwa wurin da suka yi alƙawari da Majnun. Ta kusa isa kenan ta gamu da wani mutum ya ce mata, "Yarinya kada ki je wurin nan da kika nufa. Akwai wata fatalwa mai kamar bishiya da ta bayyana."


Kullum tana kiran sunan "Laila, Laila." Da ta ji haka sai ta tabbatar Majnun ne bai tafi ba. Ta ƙarasa wurin da gudu. Yana ganinta ya yi zumbur ya miƙe tsaye yana mai farin ciki, yana cewa "Laila kin cika alƙawari? Laila ke ce kuwa? Laila za ki aure ni??" 


Kasancewar ya jima sosai a zaune ba ya miƙewa, sai jiri ya ɗebe shi, a lokaci guda kuma zuciyarsa ta buga saboda tsanannin farin ciki. Kansa ya gwaru da dutse ya faɗi sumamme.


Laila na ganin irin wannan sadaukantarwa ta kasa haƙurcewa, zuciyarta ta raurawa, ƙirjinta ya yi matuƙar ƙunci. Nan take numfashinta ya ɗauke ta faɗi a wajen sumammiya ita ma.


Kays Majnun shi ne ya fara farfaɗowa daga sumar da suka yi gabaɗayansu, ya yunƙura da zummar isa inda Lailan take amma sai ya kasa yunƙurawar saboda ba kuzari a tare da shi, cikin wata murya ma'abociyar raurawa ya ƙwalawa Laila kira "Laila...!" shirun da ya biyo baya shi ne ya tilasta masa fara jan jiki a kwancen, a hankali yana jan jiki har ya ƙarasa inda Lailar take a kwance a sume.


Cikin ruɗewa da firgici Majnun ya ringa kiran sunan Laila ganin ba ta ko alamar motsi, ya ce "Kada ki tafi ki bar Majnuninki a cikin azabtacciyar rayuwar da gwara mutuwa da ita, kin sani cewa Majnun da son ki yake rayuwa Laila..." ya ƙarashe kalaman nasa da wasu daɗaɗan baitoci:


Rabuwa da ke ba daɗi na ji a jikina.


Kar ki bar ni Lailata domin kuwa ke ce jin daɗina...'


Farin ciki ne mara misaltuwa ya bayyana ƙarara a fuskar Majnun dai-dai lokacin da ya ga Laila ta motsa.


A dai-dai lokacin da Lailar ta motsa har ma ta samu ta zauna, kuma a lokacin ne iyayen Lailar suka ƙaraso wajen da suke, iyayen Lailar suka ruɗe ganin yadda suka ga 'yarsu a wani mawuyacin hali.


Suka ɗauki 'yarsu da zummar tafiya da ita wani garin daban wanda yake da nisa daga wannan nahiyar, ''Laila..." Majnun ya ƙwala mata kira da ƙarfi ganin har sun fara yin nisa daga wajen da suka bar shi a kwancen, ƙwala mata kiran da ya yi shi ne ya yi sanadiyar ƙara dakusar da ɗan ragowar kuzarin da ke tare da shi, don haka yana gama ƙwala mata kiran sai ya kuma kifewa a ƙasa sumamme.


DUBA WANNANAsalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (4)


Laila tana ganin hakan sai ta ruɗe, ta kufce daga hannun iyayenta ta rugo izuwa gare shi.


Za mu ci-gaba Insha Allah.

Friday, 11 October 2024

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (4)

Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (4)

Lokacin da Laila ta kufce/kuɓce daga hannun mahaifiyarta kaitsaye sai ta ruga izuwa rabin ranta wato Kays Majnun kenan wanda yake kwance a sume sakamakon ƙunci da rashin ƙarfin jiki da ke addabarsa.


Ainihin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila
Hoto: Hamidsamejo

Marubuci:- Auwal Ilyas Adam


Tana isa gare shi sai ta durƙushe tana kuka gami da ambaton sunansa cikin wata murya mai ɗauke da sautin tausayi, shiru Majnun bai ko motsa ba balle ta sa ran zai amsa mata kiran nata, cikin shashsheƙar kuka Laila ta fara rerawa masoyinta wasu baitoci irin na masoya:


"Idaniyata tana ta zubar da ruwan hawaye.


Tafiyata ta zama tamkar ta masu maye.


Ga idanuwana a buɗe har gari ya waye.


Zuciyata ta soye.


Ka taso na gan ka rabin raina........."


Ganin har yanzu masoyin nata bai farfaɗoba sai zuciyarta ta karye, jikinta ya yi sanyi nan take ta faɗi a wajen da kalmar Majnun a bakinta.


A haka iyayen Lailar suka ƙaraso wajen da suke, suka ɗauke ta suka tafi da ita, suka bar Majnun kwance a sume a wajen.


Wata iska ce mai ƙarfin gaske ta ringa kaɗawa a ilahirin dajin da Majnun yake kwance, jim kaɗan da fara iskar kuma sai yanayin garin gabadaya ya canza kala, wanda hakan yake nuna cewa ruwan sama na gaf da sauka. Ruwan saman da ya fara sauka da ƙarfin gaske shi ne ya zamo silar farfaɗowar Majnun daga dogon suman da ya yi, yana farfaɗowa ya fara da kiran Laila!


Da rarrafe da jan jiki Majnun ya samu ya koma jikin bishiyar da yake ƙarƙashin ta dan dai ya tsira daga dukan ruwan saman, wasu zafafan hawaye ne suke sintiri daga ƙwayar idanunsa zuwa kan kumatunsa, gabadaya duniyar ta yi masa zafi gami da duhu, shin a ina zai ga Lailarsa ne? Me ya sa mutane suke masa kallon mahaukaci saboda kawai ya zurfafa a begen masoyiyarsa, me ya sa iyayen Laila ba sa jin tausayinsa ne? 


A haka ya kasance yana ta kuka da sambatu na rashin sanin ina zai ga Lailarsa har ruwan saman ya ɗauke, yana nan zaune sai ga wasu Fatake za su wuce sai suka ga Majnun kamar wani tsohon mahaukaci saboda gabaɗayansa ya canza kamar ba mutum ba. Fataken suka tsaya domin taimaka masa, Majnun ya kwashe labarinsa kaf shi da masoyiyarsa ya labartawa waɗannan fataken, koda fataken nan suka ji wannan labarin nasu sai suka cika da mamaki gami da tausayi, da yawa daga cikinsu suka ringa kuka saboda tsabar tausaya masa.


Majnun ya nemi fataken da su ba shi aron alƙalami da takarda zai rubutawa masoyiyarsa wasiƙa ya ba su su tafi da ita ko Allah zai sa su samu labarinta.


Suka amince da hakan kuma suka ba shi abin rubutu da takarda, ya karɓa ya fara rubutawa masoyiyarsa wasiƙa kamar haka:


"Zuwa ga wacca jin daɗin raina ya rataya a cikin ƙwayar idanunta, ki sani cewa Majnun ɗinki ba zai iya rayuwa ba idan ba da ke ba, zuciyata ta kurumce ba ta ji kuma ba ta gani matuƙar dai ni da ke za mu ci gaba da rayuwa a ware, ina mai baƙin cikin sanar da ke cewa ruhina yana gaf da barin gangar jikina mutuƙar dai na ɗau lokaci ban gan ki a kusa da ni ba Laila! Ki sani ya ke wadda farin cikina yake kai kawo a tare da ke ba zan gusa daga inda kika bar ni ba har sai ajalina ya riskeni a wajen". 


Bayan Majnun ya gama rubuta wasiƙar sai ya matsa can ƙasan wasiƙar ya rubuta wasu baitoci masu tsuma zuciyar duk wanda ya ji su:


"Yaushe ne za mu gana na ji sautin muryarki?


Zuciya sai tai ta kuka idan na duba ban gan ki ba.


A rayuwa idan babu ke ban san ni yaya zan yi ba.


Ina son jin kalamanki, ki ambata su gare ni ko zan samu haiba.


Ina ta kukan rashinki, ki tausaya min ki zo ki duba.


Ni da ke nake alfahari, Laila ki taho gare ni na bar ƙuncin zuciya......"


Fatake suka yi sallama da Majnun, fuskokinsu cike da tausayinsa, kuma suka yi masa alƙawarin Insha'Allahu za su sada wasiƙarsa ga masoyiyar tasa.


Bayan iyayen Laila sun tafi da ita, da suka isa masaukinsu sai aka yayyafa mata ruwa ta farfaɗo, tana farfaɗowa ta fara kuka gami da ambaton sunan Majnun, hankalin iyayenta ya tashi ganin ita ma ta fara bayyana duk wasu alamomi da Majnun ɗin yake nunawa a kanta, wato alamun hauka.


Iyayen Laila suka yanke shawara a kan su nufi can wajen ƙasar Bagadada domin yin ƙaura gabadaya daga yankin da 'yarsu za ta kuma ganin Majnun.


Nan da nan suka haɗa kayansu sai Bagadada, yayinda ita kuma Laila take kwance cikin matsananciyar rashin lafiya.


Kwanci tashi Fataken nan masu ɗauke da wasiƙar Majnun zuwa ga masoyiyarsa suka iso wani wuri wanda nan ne mahadar Fatake, daga wannan mahaɗar zuwa cikin ƙasar Habasha tafiya ce ta rabin kwana, wannan ne ya sa duk waɗanda suka zo da zummar shiga ƙasar Habasha sai sun tsaya a wannan mahaɗar domin kinkintsawa.


Jikin Laila sai ƙara tsananta yake, hakan ne yasa tafiyar tasu ba ta sauri, a hakan su ma suka samu suka iso wannan mahaɗar, a wannan mahaɗar suka yada zango kuma suka duƙufa nemawa 'yarsu magani, suka bada cigiya a wannan mahaɗar ko akwai mai maganin da zai iya warkar da 'yarsu, suka alƙawarta dukiya mai tarin yawa ga duk wanda ya yi nasarar warkar da ita, a shelar da aka yi sai karaf a kunnuwan waɗannan Fataken, wato waɗannan waɗanda suka ba wa Majnun magani, don haka jin an ce za a bada dukiya mai yawa sai suka je suka ce za su gwada warkar da Laila ɗin, yayin da aka kai su inda Lailar take sai aka labarta musu dalilin rashin lafiyartata.


Suna jin haka sai suka gane cewa lallai ita ce wadda Majnun ya labarta musu ita.


Fataken suka nemi da a bar su daga su sai ita a ɗakin domin a cewarsu akwai ma shafar jinni/aljanu a tare da ita, bayan an bar su daga su sai ita, sai suka labarta mata labarin masoyinta Majnun, nan da nan sai ta tashi zaune jin an ambaci Majnun ɗinta, bayan ta gama karanta wasiƙar da Majnun ya aiko mata da ita sai ta fashe da kuka, kuka mai ratsa zuciyar mai sauraro, anan Fataken suka rarrasheta da ƙyar sannan suka kwatanta mata nahiya da kuma wurin da suka baro masoyin nata.


Lokacin da iyayen Laila suka dawo ɗakin sai suka tarar da 'yarsu har ma ta tashi zaune kuma ga fara'a a fuskarta, nan take iyayenta suka nuna farin cikinsu sannan suka kawo dukiya mai tarin yawa suka ba wa Fataken nan kamar yadda suka alƙawarta.


Bayan kwana biyu da samun lafiyar Laila sai iyayenta suka yanke shawarar haɗa kayansu domin shiga cikin ƙasar Habasha, a lokacin da suka gama shirinsu kaf domin fara tafiyar, a lokacin ne kuma Laila ta sulale da taimakon wani mutum da ya sata a hanya kana ya samo mata doki ta bar nahiyar da nufin isa ga masoyinta, masoyinta na gaske wanda take da tabbacin har abada ba za a samu masoyi kamarsa ba.


DUBA CI-GABAN ANAN: Asalin Labarin Soyayyar Majnun Da Laila (5)


Kwanci tashi, ta yada zango anan ta yada zango a can har ta shigo nahiyar da Majnun ɗinta yake, don haka sai ta ƙara ƙaimi domin ta kai ga rabin ran nata, gabaɗaya kamanninta ya sauya, tayi futu-futu da ita, kuma ta rame da ma kuma gashi ba ta daɗe da farfaɗowa daga rashin lafiya ba.


Za mu ci-gaba Insha Allah.