Showing posts sorted by relevance for query LITTAFIN KIMIYYAR AURE. Sort by date Show all posts
Showing posts sorted by relevance for query LITTAFIN KIMIYYAR AURE. Sort by date Show all posts

Friday, 4 June 2021

Hikimomin Yin Aure Guda 13

Hikimomin Yin Aure Guda 13

Komai ka gani na rayuwa yana ƙunshe da fa'ida da hikima, ko a addinance, ko a hankalce, ko a al'adance, za mu kalli aure ta waɗanan ɓangarori guda uku. Na ɗaya a addinance.


HIKIMOMIN YIN AURE


MarubuciSheikh Aminu Ibrahim Daurawa


HIKIMOMIN YIN AURE DAGA LITTAFIN KIMIYYAR AURE


1.Yin biyayya ga umarnin Allah, wanda acikin haka akwai rabon duniya da lahira.


2. Biyayya ga Annabi (S.A.W), saboda aure ya tabbata a sunna ta fuska uku, ya yi umarni a yi aure, ya yi aure, kuma ya tarar ana aure, ya tabbatar tare da yin wasu gyare-gyare.


3. A cikin yin aure akwai toshe kafar sheɗan, ta kallon abin da ya haramta ko wajan faɗawa zina ko maɗigo, ko liwaɗi ko neman dabba, ko amfani da hannu, ko sauran hanyoyi na sheɗanci


4. A cikin aure akwai biyan sha'awa ga ma'aurata da kuma samun lada


5. A cikin aure akwai rage yawan ƴanmata da zawarawa, a cikin al'umma, wanda yawan su tare da samari ba tare da aure ba, sai yana barazana gamai da ɓarkewar annoba, ta zinace - zinace, haka kuma yana kawo cututtuka da saukar fushin Allah, wanda ya hana kusantar zina.


6. A cikin yin aure akwai samun zuriya, wacce za a yi mata tarbiyya mai kyau a gaban uwa da uba da renon al'umma ta gari. 


7. A cikin aure akwai samun nutsuwa da kwanciyar hankali, da soyayya tsakanin miji da mata. 


Manzon Allah (S.A.W) yace "Babu abin da ya dace da masoya irin su yi aure.".


8. A cikin yin aure akwai samun lada mai yawa wajan ciyar da iyali da ɗaukar nauyin su da sauran hidimomin su na yau da kullum, duka yana shiga cikin sikelin lada na mutum a ranar alƙiyama.


9. A cikin aure za ka samu jari na ɗa ko ƴa ta gari wacce za su dinga yi maka addu'a ko bayan mutuwar ka, ka bar sadaƙa jariya.


10. A cikin aure akwai idan ka haifi ƴaƴa suka mutu su na ƙanana, za ka amfana da su ranar alƙiyama, kamar yadda ya tabbata a hadisi.


11. Idan mutum ya yi aure sai Allah ya ba shi ƴaƴa mata daga biyu zuwa sama, ya tsaya ya kula da tarbiyyar su, da dukkan buƙatun su na ilmi, da tarbiyya, da lafiya da sutura har suka girma ya yi musu aure, Aljanna ta tabbata a gare shi. Kamar yadda ya tabbata a hadisi. 


12. Aure yana kare addini wanda ya yi aure ya cika rabin addininsa, ya ji tsoran Allah shi ne cikon rabin. (Hadith). da rayuwa yana hana yaɗuwar cutaka masu kisa kamar HIV, da mutunci, an fi ganin mutuncin masu aure ko da kuma marasa auran su na da mutunci. da hankali domin da yawa marasa aure su na samin ciwon hauka saboda zaman kaɗaici da takaici da rashin abokin zama yake haifarwa. Da dukiya yin aure yana tsare yawan shan magunguna na ƙarya sha'awa da wahalar siyan abinci. da nasaba, domin yana tsare yaɗuwar fyaɗe da zina, a cikin al'umma da ƴaƴan shegu, duk da ba laifin su bane. 


13. A cikin littafin ihya'u ulumidden. 2/72 na Al'imam Garzali, ya kawo ƙissar wani bawan Allah, wanda ake bashi shawara ya yi aure tunda yana da halin riƙe matar sai yaƙi yi. Bayan ɗan wani lokaci sai ya kwanta bacci, yana tsakar bacci sai aka ga ya tashi a firgice yana cewa, don Allah ku aurar da ni, sai aka ce masa mai ya faru? Sai yace "Na yi mafarki a cikin wannan baccin alƙiyama ta tashi, muna tsaye cikin damuwa da baƙin ciki ga ƙishrwa mai tsanani, muna ciki sai ga wasu yara su na ɗauke da wasu fitilu masu haske, da kofuna a hannun su na zinarai da azurfa, su na shiga cikin mutane su na ba wa wasu daga ciki ruwa, su na tsallake wasu sai nace ku taimake ni da ruwa ina jin ƙishrwa mai tsanani, sai suka ce ai baka da ɗa a wannan wajan, mu muna shayar da iyayan mu ne waɗanda suka haifemu, muka mutu kafin su.". 


Ya ce wannan shi ne dalilin da yasa nace kuyi mini aure, ko Allah ya azurtani da ɗa na gari da yi mini addu'a idan na mutu, idan kuma ya riga ni mutuwa ya taimaka ni a wannan wajen.


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin

aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.

Thursday, 5 January 2023

Hukunci Tare Da Muhimmancin Yin Aure Ga Musulmai A Addinin Musulunci

Hukunci Tare Da Muhimmancin Yin Aure Ga Musulmai A Addinin Musulunci

Yin aure, abu ne da ya dace da  shari'a da lafiyayyan hankali da al'ada mai kyau. Akwai hikimomi da fa'idoji masu tarin yawa wajan yin aure, ga maza da mata, Allah ta'ala ya ce: (fassara) "Su matanku tufafi ne a gareku kuma tufafi ne a gare su.". Suratul Baƙara. 


Muhimmancin Yin Aure Ga Musulmai
Hoto: About Islam


MarubuciSheikh Aminu Ibrahim Daurawa


AURE A INUWAR MUSULUNCI DAGA LITTAFIN KIMIYYAR AURE


Wannan  aya ta nuna aure ado ne kwalliya ne, sutura ne rufin asiri ne mutuncin ne da daraja, saboda yadda aka kamanta rayuwar ma'aurata da tufafi, yadda tufafi suke ga Ɗan Adam, suna da amfani da yawa don haka aka kamanta rayuwar aure da tufafi, daga ciki amfanin tufafi akwai rufe tsiraici da yin kwalliya, da sutura, kuma duk wanda zai ɗinka tufafi yana buƙatar yasan kalar yadin da zai saya, na auduga ko na kattani ko na roba, mai kauri ko mai shara-shara,  mai tsada ko mai arha ko tsaka-tsaki,  fari ko baƙi ko wata kala daban, sannan wajan ɗunki mai yalwa ko mai matsi, ko kadaran kadahan, to haka rayuwar aure take wajan zaɓin abokin zama.


HUKUNCIN YIN AURE


Kasancewar mutane sun bambanta a halitta da halaye da yanayi, yasa malamai suka kalli ayoyi da hadisai da suka yi kira akan yin aure suka ba su fassara kashi uku:


Wasu malamai suna ganin yin aure sunna ne, abin da suke nufi, idan ka yi aure za ka sami lada, amma idan ba ka yi aure ba, kuma ba ka yi fasiƙanci ba, ba ka da alhaki. Wannan shi ne ra’ayin mafi yawan malamai, Badayatul mujtahid na Ibn Rushed 2/23. Addasuƙiy 2/214. Almugniy 6/446.


Na biyu sun ce yin aure sau ɗaya a rayuwa wajibi ne ga mutum, idan ya zauna bai yi aure ba ya yi laifi, domin wajibi shi ne abin da shari'a ta nemi ayi shi dole, idan mutum ya yi yadda aka umarce shi zai sami lada, idan kuma yaƙi ya zama abin zargi, kuma ana iya yi masa uƙuba akan haka. Saboda ko ba komai aure yana cika kamalar mutum mace ko namiji. Kuma abubuwan da suke cikin aure suna da yawa na buƙatu tsakanin namiji da mace, don haka idan aka yi aure kowa zai amfana. Wata ruwaya daga Alimam Ahmad, da wasu manyan Malamai daga cikin magabata, Almuhallah na ibn Hazamin, 9/440. Fathul Bariy 9/110. Dauda azzahiriy, Ibn Hazamin.


Na uku suka ce shi aure ya kasu gwargwadon yadda mutane suka karkasu;


Na ɗaya wanda aure ya zama wajibi a kansa. (shine wanda yake da ƙarfin sha'awa kuma yana da halin da zai iya riƙe auran ko sana'a, kuma idan bai yi auran ba zai yi lalata.).


Na biyu wanda aure ya zama sunna akansa. Wanda zai iya ɗaukar nauyin iyalin kuma yana yin wata sana'a ko neman ilmi, ba shi da sha'awa mai ƙarfi).


Na uku wanda aure ya zama haramun akansa. (Wanda ba zai iya ɗaukar nauyin matar ba, kuma ba shi da buƙatar auran, ko idan ya yi zai dinga cutar matar, wajan hana ta haƙƙoƙinta, ko ba shi da lafiya wajan biyan buƙatar iyali).


Na huɗu wanda aure ya zama makruhi akan sa. (ba a so ya yi aure saboda ya shagala da wani abu mai muhimmanci, ko ibada ko wani ilimi, ko wani bincike wanda ya hana shi samun lokaci, ko kuma ba shi da sha'awa, kuma babu tsoran yin lalata tare da shi.).


Na biyar wanda aure ya zama halal a gare shi (idan ya yi babu matsala, idan bai yi ba babu matsala).


Wannan shi ne magana Malikiyya, kuma akwai irin wannan ya shahara a fatawar daga wasu cikin shafi'awa da Hanbaliya. Fathul Bariy 9/110. Alƙawaninul Fiƙhiyya Ibn Juzay. 193.

 

Wannan shi ne fassara da malamai suka bayar ga dukkan ayoyi da hadisai masu kira da yin aure.

 

Amma ba kowa ya kamata ya yi aure ba saboda wasu ba su da sha'awa wasu ba su da lafiya wasu ba su da hali wasu ba su da lokaci, wasu kuma sun shagala da wani abu da ya fi yin auran muhimmanci a wajan su a wannan lokacin, kamar yadda Shaikh Abu Gudda ya kawo tarihin wasu malamai maza da mata waɗanda har suka gama rayuwar su ba su yi aure ba, yawan ya haura talatin, a cikin littafinsa mai suna Al'ulama'ul Uzzab.


Haka kuma ba kowa zai ƙi yin aure ba, domin wasu suna da buƙatar yin auran, domin samun zuriya, wasu domin samun abokin rayuwa wasu domin kare kai da gujewa lalata, kamar zina, maɗigo da luwaɗi, wasu domin ƙara mutunci da kamala.

Wednesday, 13 November 2024

Sirrin Yadda Ake Neman Aure A Musulunci

Sirrin Yadda Ake Neman Aure A Musulunci

Zaɓar abokin zama a aure ya fi kowane zaɓe wahala da haɗari, domin idan mutum ya tafka kuskure, ko ya bi son zuciya, to ya shiga matsala kenan har ƙarshen rayuwar sa, shi ya sa ake buƙatar ilimi da wayewa da bi a sannu kafin yanke shawarar fitar da abokin rayuwar aure, saboda kusanci da sirrin da ke tsakanin mace da mijin ta.


Sirrin yadda ake neman aure a musulunci
Hoto: Easy peasy

MarubuciSheikh Aminu Ibrahim Daurawa


HIKIMOMIN YIN AURE DAGA LITTAFIN KIMIYYAR AURE


Alaƙa tsakanin mace da namiji alaƙa ce mai tushe, Allah ta'ala ya gaya mana matakai uku a cikin ayar farko ta suratun nisa'i, na ɗaya, ya halicci 'Yan Adam daga Annabi Adam (A.S), mataki na biyu ya halicci matar sa daga gare shi, na uku daga gare su ya samar da dukkan maza da mata, don haka soyayya da ƙauna da bege da shauƙi da ke tsakanin su na reshe ne da tushe, an ce saboda sanin asali ya sa kare ya ci alli.


Don haka mace ta na buƙatar namiji kamar yadda namiji yake buƙatar mace, kowanne yana da abinda ɗayan ba shi da shi, wanda kamalarsa da mutuntakar sa, da buƙatar sa ta jingina ga abokin tarayyar sa.


Aure abu ne mai mahimmanci a rayuwa kuma wani babban canji ne a rayuwar mutum, idan ya yi kuskure ko ganganci, ya lalatawa kansa wani ɓangare mai girma na rayuwar sa don haka a nutsu sosai a bi ƙa'ida domin kaucewa nadama.


Zuwa zance ko ganin mace domin gabatar mata da kai, a matsayin mai neman aure, shi ne abin da malamai suke kira neman aure ko kuma kiɗbah, asali ana neman auran mace a wajen waliyinta a mataki na farko domin samun iznin ganin ta da tattaunawa da ita, don samun fahimta, kamar yadda Manzon Allah (S.A.W) ya nemi auran Aisha a wajen mahaifinta Abubakar. Bukhari 5081.


Mataki na biyu, ana iya neman auran mace kai tsaye a wajen ta idan mai hankali ce, kamar yadda Annabi (S.A.W) ya nemi auran Ummu Salamata a gurin ta, har ta bayar da uzurin yawan 'ya'ya da shekaru da tsananin kishi, ya ba ta amsa da zai riƙe mata ƴaƴan, shekaru kuma shi ma yana da su, kishin kuma zai roƙi Allah ya rage mata shi, Muslim Annasa'iy.


Mataki na uku mahaifin mace ko waliyinta zai iya gabatar da ita ga mutanen kirki, domin sama mata miji, kamar yadda S. Umar ya gabatar da 'yarsa Hafsah ga S. Abubukar, sannan Usman daga baya Manzon Allah (S.A.W) ya aure ta. Bukhari 5122. Da hadisin Umma Habibah da ta nemi Manzon Allah (S.A.W) ya auri ƴar'uwarta, ya nuna mata ba ya hallata a musulunci haɗa 'yan'uwa a igiyar aure ɗaya a lokaci ɗaya. Bukhari 5107.


Mataki na huɗu ya halatta mace mai hankali ta gabatar da kanta da wani mutum nagari ko zai amince ya aure ta, kamar yadda wata mata ta gabatar da kanta ga Manzon Allah (S.A.W) ko zai amince ya aure ta, Bukhari 5120. 


Mataki na biyar wani ya na iya zama sila ko dalili wajen shige wa gaba wajen ƙulla alaƙar aure tsakanin masu neman aure kamar yadda kaulatu Bnt Hakeem ta gabatarwa da Manzon Allah (S.A.W) auran Nana Saudah bayan wafatin mijinta. 


Mataki na shida za a iya kafa wata ƙungiya mai ɗauke da amintattun mutane masu ilimi da sanin haliyyar jama'a, su ɗinka zama masu dalilin aure, duk mai neman aure mace ko namiji sai ya je gurinsu, domin tantancewa da shigewa gaba wajen haɗa aure.


Mataki na bakwai za a iya buɗe wata kafa a yanar gizo, domin wannan aiki amma yana buƙatar aiki da saka ƙaidoji domin kada a canja munufar buɗewar zuwa wani abu daban.