Friday 25 May 2018

KARANTA YANZU KAJI: TAKAITACCEN TARIHIN SARKIN KASAR MOROCCO MOULAY RASHID ISMA'IL

Tura Wannan Zuwa
Marubuchi Sadiq Tukur Gwarzo, RN.
08060869978

An haifi Moulay Ismail Rashid a wajajen shekarar 1646 a birnin Fez na kasar Morocco. Ya gaji mulkin Morocco ne tun yana da shekaru 26 a duniya bayan da ɗan uwansa mai mulki ya faɗo daga kan doki ya mutu.



A wancan lokacin Moulay Ismail ya samu daular Moroco rarrauna saboda yawaitar faɗace-faɗace tsakanin kabilu gami da rikicin sarauta da yayi tsamari a daular. Baya da haka ma, birnin Marrakesh yayi bore ga shugabancinsa, inda mutanen garin suka shiga biyayya ga ɗan amminsa mai suna Ahmad ibn Muhriz.

Don haka da fara mulkinsa, sai ya jagoranci runduna zuwa Marrakesh dake kudancin birninsa, ya faɗawa garin da yaki har kuma yaci nasarar kwace ikonsa, amma sai shugaban boren Ahmad bn Muhriz ya tsere ba tare da an kame shi ba.

Sarki Moulay Ismail na ɗaya daga cikin sarakuna masu karfin iko waɗanda duniya ba zata taɓa mancewa da sunansu ba.
Da fari dai, ya ɗauke cibiyar daularsa daga birnin Fez zuwa Meknes, sannan ya umarci a kawata ganuwar birnin da kawunan sojojin abokan hamayya guda dubu goma.

Ance akalla a kusan shekaru hamsin dayayi yana mulki, ya kashe mutane sama da dubu talatin waɗanda yawancinsu barorinsa ne, ɓata masa rai sukayi kurum, ko kuma ace lalacinsu ne ya isheshi sai yasa a kashe su.
Wasu kuma ya sanya a kashe sune saboda ayyukansu bai gamsar dashi ba. Domin ance shi makarancin littafin alkurani mai girma ne, kuma indai yana bisa doki, yana umartar barori su bishi ɗauke da alkurani a buɗe yana mai karantawa, amma fa da zarar sun aikata abinda ya sosa masa rai sai ya sare kawunansu.

Sarki Moulay Ismail ibn Sharif ya shahara wajen gwabza yakuna da makwabtansa, sannan ya ciri tuta wajen kawata babban birninsa, domin shine sarkin daya umarci ayi gine-gine masu kayatarwa a birnin Meknes, misalin makarantu, masallatai, lambuna da wuraren hutawa da kuma ganuwa ga wannan birni.

Haka kuma yayi gagarumin faɗa da daular Ottoman wadda cibiyarta ke kasar Turkiyya, anan ne har ya samu nasarar 'yantar da kasar Morocco daga karkashin wannn daula.

A shekarar 1981 Sarki Moulay Ismail ya gwabza yaki da turawan Kasar Spain tare da karɓe ikon birnin 'La Mamora' mai ɗauke da tashar teku, inda ya sauyawa birnin suna izuwa al Mahdiya.

A lokacin wannan yaki, wakilin sarkin mai suna Kaid Omar ya faɗawa Sifaniyawan cewa idan suka mika wuya ba zasu bautar dasu ba, wanda hakan ya karfafa musu guiwar dakatar da gwabza yaki bisa tsammanin samun adalci, amma bayan anci nasara, sai Sarkin yaga cewa sam ba zai iya barin sifaniyawa sama da dubu biyu masu ɗauke da kyawawan mataye da kayayyaki masu daraja ba sasakai, sai kawai ya bada umarnin a taso keyarsu zuwa birnin Meknes a matsayin ganimar yaki.

A shekarar 1684 Moulay Ismail ya kwace ikon birnin Tangier wanda a lokacin turawan Portugal ke iko dashi, haka kuma a shekarar 1689 ya sake karɓe ikon wani babban birni mai suna Larache daga hannun turawan sifaniya.

Bunkasar wannan sarki takai yadda sai daya tara rundunar mayaka bakaken fata mai ɗauke da akalla soji dubu goma sha biyar, dasu ya haɗa da nashi wajen yaki ta yadda sai daya karɓe ikon ɗaukacin kasar Morocco daga hannun turawa idan aka ɗauke yankunan Ceuta da Melilla.

Akwai labaru masu nuna gwagwarmayar daya buga da faransawa, tunda ance ya kame wasunsu masu zuwa leken asiri kasarsa tare da mayar dasu bayi, amma wasu na ganin kasancewar a lokacin sarkin Faransa Louis na 14 yana kiyayya da Sipaniyawa, ance akwai zumunta maikyau a tsakaninsa da Sarkin na Meknes.

An kuma ruwaito cewa Sarki Moulay Ismail na Morocco ya taɓa aikewa da jakada mai suna Muhammad Temimin domin nema masa auren gimbiyar Faransa mai suna Marie Anne de Bourbon amma sai taki amincewa, sai dai duk da haka alaka mai kyau taci gaba da ɗorewa a tsakaninsu.
A iya tsawon rayuwar Sarki Moulay Ismaïl, ance ya haifi 'ya'yaye guda 867, maza guda 525 da mataye 342. Ance baya da mataye guda huɗu da yake dasu, akalla yana da kuyangi guda 2,000, kuma an ƙlisssafta cewar a kalla a tsawon shekaru tamanin da yayi a raye, a shekarunsa sama da hamsin bisa karagar mulki akullum yana jima'i sau biyu, ko kuma da mataye guda biyu.

Don haka sunansa ya shiga tarihi a matsayin wanda yafi kowanne namiji yawan haihuwa anan duniya a iya abinda ya fito ga sanin masana zuwa yau.

Bayan rasuwar Moulay Ismaïl a shekarar 1727, rikici ya kara ɓarkewa tsakanin 'ya'yansa bisa wanda zai gajeshi a mulki, daga karshe wani ɗansa Muhammad yayi galaba, tare da ɗorawa akan gine-ginen da mahaifinsa ya soma. Sai dai girgizar kasar data auku a birnin Meknes cikin shekarar 1755 ce ta lahanta kusan ɗaukacin waɗannan gine-gine, daga karshe tilas Sarki Muhammad ya ɗauke cibiyar birnin daga nan inda ya maida ita zuwa birnin Marrakesh.

Macen da tarihi ya kiyaye a matsayin wadda tafi kowacce yawan haihuwa itace Mrs Vassillev ta birnin Moscow, wadda ta rayu tsakanin shekarun 1725 - 1765. Ance tayi nakuda sau 27, sau 16 tana haihuwar tagwaye, ta haifi 'yan uku sau bakwai, ta haifi 'yan huɗu sau huɗu. Jimilla ta haifi 'ya'yaye 69 reras.. (Kimiyya ta tabbatar da haka)

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin aiki Tukuru don jin dadin ku Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin website din akwai "Home" sai ku shiga,

mungode

Muryarhausa24.com Zata Kasance Babbar Kafar Yada Labarai aduk fadin Duniya domin Bunkasa Harshen Hausa, domin Zafafan Labarai ziyarci www.muryarhausa24.com

Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com

Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin Muryarhausa24.com aduk inda kuke a fadin Duniya farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24.com shine ta fito da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi
me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@
gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki daya Amin

Source by ©Muryarhausa24.com
TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user