Monday 25 September 2017

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Adamawa Ya Tsallake Rijiya da Baya

Tura Wannan Zuwa

Guguwar tsige-tsige da ta ratsa majalisar
dokokin jihar Adamawa ta rutsa da duk
shugabaninta sai kakakin majalisar Kairu
Mijinyawa da ya sha da kyar

A zaman majalisar a wannan Litinin kakakin
majalisar wanda ya jagoranci zaman majalisar,
Kabiru Mijinyawa, ya tsallake rijiya da baya,a
guguwar tsigau din ,to amma kuma mataimakinsa
Sunday Peter da sauran shugabanin majalisar
basu taki sa’a ba, inda yan majalisa 17 cikin 25
suka kada kuri’ar tsige su.
Cikin dai wadanda suka rasa kujerun nasu baya
ga mataimakin kakakin majalisar sun hada da
shugaban masu rinjaye,da mataimakinsa,da na
marasa rinjaye da gagara badau din majalisar.

To wai ko me yayi zafi da yan majalisar suka
dauki wannan mataki a yanzu? Hon.Hassan
Barguma shine sabon shugaban masu rinjaye na
majalisar ya bayyana dalilansu na daukan
wannan matakin tsigewan inda yace sun dau
matakin ne don kawo gyara.
To sai dai tuni wannan sauyi ya soma jawo
cecekuce inda wasu ke zargin cewa da hannun
bangaren zartaswa a wannan tsigewa,koda yake
gwamnan jihar Sen.Muhammadu Bindow Umaru
Jibrilla ya musanta zargin cewa da hannunsa a
wannan satoka-sa-katsin.

Gwamnan ta bakin daya daga cikin hadimansa ta
fuskar harkokin yada labarai Danjuma Bakari
(wato Danjuma Hamas),yace babu hannunsa a
ciki.
Suma masana harkar majalisa irinsu
Hon.Abdulmumini Ibrahim Song,tsohon dan
majalisar dokokin jihar na ganin akwai abun
dubawa game da wannan sauyin daya kada a
majalisar.

Koma da menene dai yanzu an zura ido a ga
yadda zata kaya,yayin da masu fashin baki ke
cewa lokaci ne kawai ke iya tabbatar da abun da
ka iya faruwa.

.
Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa kamar haka  dadinkowa24.blogspot.com mungode
.
Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa nayau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com
.
Idan kana/kina da Labarin daku keson asanarwa da Duniya, ko Tambaya,Shawarwari,Hausa Novels, Nishadantarwa,Ilimantarwa,Ko Neman Sani akan ranakun dazamu cigaba dakawo muku Posting na Hausa Novels da Sauran su, zaku iya tuntubar ma'aikatan mu kuturo da Sunan Ku tareda Addreshin Ku tawannan Email din Officialdadinkowa24@gmail.com kyautane zamuyi muku komai don cigaban Al'ummar Hausa bama bukatar kudinka sai dai idan kaikayi niyyar Turowa don siyan Data Saboda acigaba dayin Posting a Kodayaushe batareda dakatawa ba, Al'ummar Nigeria  daga N50 zuwa abinda yasamu duk zaku iya turo da Lambobin katin  ta Email din mu akan officialdadinkowa24@gmail.com  ko Neman Account Number din mu na Bank ga mutanen dabasa cikin Nigeria, Website din Mu bashi da Alaka ta kusa ko tanesa da Wani/Wata Dan Siyasa/'Yar Siyasa afadin Duniya Burin mu shine musamu amincewar Al'umma aika da Gudunmawarka,Labari,Shawara da sauran su a Addreshin mu na email ✉💌📩 officialdadinkowa24@gmail.com 
.
Suna addreshin misali..
.
Subject: Fatan Alheri
Suna: Yusuf Tk
Kasa: Nigeria
Gari: Kano
Garin da akeda Zama: Kaduna
Sako: Yaushe Ne zaku cigaba da Labarin Kundin Tsatsuba Littafi na 2 na Madakin Gini? Mungode
.
Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com
.
Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri
.
ALLAH yabar Zumunci Amin🙏
.
.
Source By ©Voa Hausa

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: