Thursday 11 January 2018

DUK MUSULMIN DAKE ONLINE YA KARANTA WANNAN-KARANTA ANATSE KAJI

Tura Wannan Zuwa

MISALI

Bayan na dauki
wani lokaci mai
tsayi ina kwance
ina bacci sai naji
matata tana ta
tashina daga bacci,
babban abinda ya
bani mamaki shine
yadda na farka
kuma nakemata
magana cewa

ME KIKE BUKATA?

Amma ita kwata
kwata batajin
maganar da
nakemata, amma
ahaka tajuya ta
fita, bayan kamar
minti 30 sai ta
dawo takara
tashina na farka
nacemata

ME KIKEBUKATA?

Amma ina batasanma
inayiba. Kawai sai
naga ta fita waje
afirgice tana kiran
‘yan-Uwana. sai
naga ‘yan-Uwana
sunkira likita yazo
gurina yana gwada
jikina, sai nacema
likitan

ME KAKE BUKATA?

Amma wani abin mamaki
sai naga likitan
bayajin maganar
da nakeyi, sai naji
likita yana gayama
‘yan-Uwana cewa
na” mutu”. Sai suka
firgita sukai tayin
koke-koke duk
dacewa
banmutuba, ni dai
bansan dalilin da
yasa basajin
maganataba, wannan
abu yayi matukan
ban mamaki
musamman da naji
‘yan-Uwana
sunacewa
“agaggauta ayi
jana’izata”, sai naga
sun daukeni
sunkaini dakin da
nake ajiye
motocina, ga shidai
inayimusu magana
amma kwata
kwata basajin
maganar da nakeyi,
sai suka ciremini
tufafina sannan
suka yimini wanka
suka samini
likkafani kuma
suka daukeni suka
kaini masallaci don
ayimini sallah. Na
samu liman na
gayamasa cewa
da raina ban
mutuba, amma sai
naga liman yaki ya
kulani inaji ina gani
sukaimin sallah,
bayan sungama
yimin sallah sai
suka daukeni suka
nufi makabarta
dani inaji ina gani
suka rika kokarin
binneni, bayan
sun sa ni acikin
kabari sai naga
wani daga cikin
‘yan-Uwana na
kusa wai har dashi
ake kokarin
binneni, sai
nacemasa

NIFA BAN MUTUBA

Dan haka karda ku
binneni, amma sai
naga ko kulani
baiyiba kamar
baisan inayimasa
maganaba, bayan
sungama zubamini
kasa sai na tuna da

Hadisin MANZON ALLAH (S.A.W)
ya ce “lallai mamaci
yanajin takun
takalman mutane
idan suka juya
zasu fita daga
maqabarta”, sai
nima narika jin
takun takalmansu
alokacinda suka
juya suka barni
acikin
kabari, wannan
shine abinda ya
tabbatar mini
cewa

AYANZU INA CIKIN WANI GURIMAI TSANANIN DUHU.

Bayan haka
sai wasu mazaje 2
masu firgitar da
jama’a sukazo
guna, 1 daga
cikinsu ya tsaya
akusa da kafafuna
1kuma ya tsaya
akusa da kaina
sannan aka
tambayeni

WAYE UBANGIJINKA?

Saina fara tunani
waye Ubngijina?
alhali nasan
Ubangijina dan
haka narika
mamakin yadda
akayi na manta,
haka da aka
tambayeni

WAYE ANNABINKA?

Nan fa na fara
tunani
ANNABINA! ANNABINA!! ANNABINA!!!

Sannan aka
tambayeni miye
ADDININKA? nanfa
nashiga tunani
addinina addinina
ga shidai nasan
amsoshin amma
abun mamaki shine
yadda na
manta, babu wani
abu da yake
fadomini arai bancin
matata da
shagona da ‘yan-Uwana da motata,
har saida naga
ansa wani katon
kulki andakeni
dashi duka mai
tsanani, nanfa na
saki baki na
kwarara ihu!

IHUN DA YA TAYAR DA
DUKKANNIN MUTANEN
GIDANMU.

Da sukeyin bacci, sai
matata ta kira
sunana sannan
tace:

MEYASA KAKEYIN IHU DA KA’RA IRIN HAKA?

Awannan lokacin
ne na gane cewa
mafarki nayi, nanfa
na tsaya inata
haki kawai sai naji
ankira sallar
asubah sai ya
zamana cewa
wannan mafarki
da nayi shine
sanadiyyar
shiriyata, tundaga
wannan ranar
narika dagewa
wajen yima ALLAH
(S.W.T) biyayya.

WANNAN KENAN gaskiya ‘yan-Uuwa Musulmai
muji tsoron ALLAH, domin watarana wannan labari zai faru akankowa wannan tunatarwace,
muna rokon ALLAH yabamu ikon amsa tanbayoyin
kabari.

YA ALLAH KADAUKI RANMU MUNA MUMINAI

Amin S. Amin

Tunatarwa daga M. Kabiru Muhammad

Shafin komai da ruwanka, Dadinkowa24 munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address
kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa
kamar haka dadinkowa24.blogspot.com

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin
Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://
dadinkowa24.blogspot.com

Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Dadinkowa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Babban Shafi a Yanar Gizo da
ke gabatar da
shirye-shiryensa a cikin harshen Hausa Zalla
cikin 24 Hours ba tareda kakkautawa ba

Burin shafin DADINKOWA24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

ALLAH yabar Zumunci Amin

Source By ©Rayuwa a Musulinci & Mujallarmu

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: