Tuesday 16 January 2018

TUNAWA DA TARIHIN MUTANEN DA SUKA GINA AREWA: SIR. ABUBAKAR TAFAWA BALEWA-Karanta Kaji

Tura Wannan Zuwa

An haifi marigayi firimiyan ƁNigeria na farko watau Abubakar Tafawa Balewa a garin Tafawa Balewa na Bauchi, a shekarar 1912.

Mahaifinsa Yakubu ɗan Zala ya fito me daga kabilar Bagire, kuma shine dagacin Lere.

Tafawa Balewa ya soma karatun alkur'ani dana boko a Bauchi, koda yake ance yaje katsina karatu, daga bisani ya samu gurbin karatu a Kwalejin Barewa ta zaria, yana kammalawa kuwa aka bashi shaidar malinta inda ya dawo Makarantar Midil ta Bauchi ya soma koyarwa.

Tafawa Balewa ya samu gurbin tafiya Ingila karo karatu tare dasu Mallam Aminu kano, inda ya samo shaidar Malanta na koyar da Tarihi acan, sannan ya dawo gida.

Da dawowarsa kuwa sai ya zamo wakilin turawan mulki masu kula da makarantu, alokacin kuma an ruwaito yana cewa ya gano yadda rayuwa take tafiya a turai cikin 'yanci da walwala, kuma ya haɗu da mutane masu bin doka ba tare da tsoron komai ba, don haka yana kallon Nigeria da wani yanayi na daban.

A lokacin ne ya soma kafa kungiyar malamai ta Bauchi, inda suke tattauna hanyoyin samar da cigaba, daga bisani kuma ya tsaya takara kuma yaci zaɓen ɗan majalisar wakilai na Arewa a shekarar 1946.

A majalisar Arewa suka haɗu da Ahmadu Bello har kuma suka kafa jamiyyar 'Northern People's Congres' watau NPC.

A shekarar 1952 tafawa Balewa ya zama ministan aiyuka, daga baya kuma ministan sufuri.

A shekarar 1957 aka naɗa shi babban minista, sannan kuma bisa haɗin guiwar jamiyyarsa ta NPC da jam'iyyar Nnamdi Azikwe, Tafawa Balewa ya zamo Firimiyan Nigeria na farko bayan karɓar 'yancin kai a shekarar 1960. Kuma ya sake tsayawa takara a shekarar 1964 ya lashe zaɓe.

Ana yiwa Tafawa Balewa lakabi da 'Golden Voice', saboda nasibinsa wurin iya zance da gamsar da mutane. Kuma a wancan lokacin, ya zamo fuskar Afirka, domin yayi aiki tukuru wajen haɗa alaka tsakanin Nigeria da kasashen Afirka, da kuma warware matsaloli tsakanin Kasashen Afirka. Sannan ya cusa 'yan Arewa da dama acikin kunshin mukaman Gwamnatin tarayya.

Akarshe, lokacin Juyin mulkin 17 ga watan janairu na shekarar 1966, ance wasu sojoji su biyar sun kutsa kai gidan sa inda suka sace shi.. Daga baya kuma aka tsinci gawar sa.

Da fatan Allah yajiqansa Amin.

Shafin komai da ruwanka, Dadinkowa24 munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address
kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa
kamar haka dadinkowa24.blogspot.com

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin
Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://
dadinkowa24.blogspot.com

Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Dadinkowa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Babban Shafi a Yanar Gizo da
ke gabatar da
shirye-shiryensa a cikin harshen Hausa Zalla
cikin 24 Hours ba tareda kakkautawa ba

Burin shafin DADINKOWA24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

ALLAH yabar Zumunci Amin

Source By ©Sadiq Tukur Gwarzo, RN.

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: