Thursday 12 April 2018

Karanta Kaji: Duk Duniya Ba Wanda Ya Isa Ya Hana Ni Zama Shugaban Kasar Nijeriya inji -Sule Lamido

Tura Wannan Zuwa

Tsohon gwamnan Jihar Jigawa, kuma daya daga
cikin masu neman Jam’iyyar PDP ta tsayar da su
neman Shugabancin Kasarnan, Sule Lamido, ya
ce, ba wanda ya isa ya hana shi zama Shugaban
kasarnan a zabe mai zuwa.

Lamido, ya yi wannan furucin ne a wajen wani
taro na bude Ofishin kamfen din shi na neman
Shugabancin kasa a Birnin Kudu, ta Jihar Jigawa.

Idan har nufin Allah ne, ba wanda zai iya hana ni
kasancewa Shugaban kasan nan. Ya kuma bayyana cewa, shakka ba bu, za a fafata
neman Shugabancin kasar nan ne a shekarar
2019, a tsakanin wadansu mutane biyu, duk
cikansu Musulmai, Fulani, tsaffin gwamnoni
sannan kuma tsaffin Ministoci a kasar nan a
lokuta daban-daban. “Kai ba bu fa wani dan adam a doron duniyar
nan, wanda ya isa ya hana nufin Allah, idan har
Allah Ya nufa ni ne zan kasance Shugaban
wannan kasar, ko ta hanyar Kotu, ko ta wace
hanya, ba wanda ya isa ya hana ni.

“Bambancin da ke Tsakani na da Buhari shi ne,
duk da ya taba zama gwamna a karkashin
mulkin Soja, amma dai bai yi wa mutane aiki ba.

Ya kuma yi Ministan Man Fetur, wanda mutane da
yawa ma ba su san hakan ba. Alhalin ni, a lokacin
da na yi Ministan harkokin waje, duk duniyan nan kowa ya sanni, sannan kuma, ayyukan da na
yi a shekaru takwas na zama na a kujerar
gwamna, sun isa shaida a gare ni. Sule Lamido, ya kara da cewa, Shugaba
Muhammadu Buhari, Bafillatani ne kadai da
sunan an haife shi Bafillatani, daganan, sai ya
kalubalanci Shugaba Buhari da ya fassara masa
wasu ‘yan kalamai da ya yi zuwa Fullanci a wajen
taron. “Buhari da Jam’iyyar sa ta APC, ba karyar da ba su
shararawa al’ummar Nijeriya ba a lokacin zaben
2015, to yanzun mutane sun san gaskiyar
lamurra, za kuma su ba su amsa a zaben 2019,” duk in ji Sule Lamido.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku
Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Muryarhausa24.com don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum

An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com
Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Muryarhausa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki
daya Amin Summa Amin.

Source by ©Hausa leadership and Hausa Class

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: