Friday 25 May 2018

KARANTA YANZU KAJI: SHIN KO KUNSAN BABBAN DALILAN DA SUKA SA AKA KAFA TASHAR TALABIJIN DIN AREWA24???

Tura Wannan Zuwa
Nazari akan tashar Talabijin ta AREWA-24




Ina ma’abota kallon wannan tasha ta
Arewa24, ina mai maku sallama irin ta
addinin muslunci. Assalamu alaikum. A
matsayina na Musulmi, kuma ‘dan
Nigeria kuma ‘dan Arewa, na zurfafa wani binci ke, (Domin ni mai sha’awar
bincike ne akan duk abinda nake ko nake
so) wanda nake ganin yana da matukar
muhimmancin dukkanin ma’abota kallon
wannan tasha su amfana da sakamakon
wannan bincike nawa. Amma yana da kyau akan duk wanda ya
karanta wannan rubutu nawa kada ya
yanke mun hukunci har sai ya karanta
rubutun tun daga farko har karshensa. Na
biyu kuma duk abinda na rubuta wanda
mai karatu bai gamsu da shi ba, to kamin ya yanke mun hukuci ina rokon sa da yayi
bincike, ko ya tambayi masana da yake
ganin suna binciken ababen dake faruwa
a duniyar yanzu, ko ma yayi amfani da
kafar bincike ta internet domin binciken
wannan jawabi nawa. Da fatar Allah ya shige mana gaba adukkanin ababen da
muka sani a fili, da kuma wadanda suke
a ‘boye. Da farko ni mai sha’awar kallon
wannan
tasha ne ta Arewa24, sakamakon suna
gudanar da shirye-shiryensu da harshen Hausa, kuma ni bahaushe ne. Haka zalika
yanayin fitar da hotonsu acikin quality
mai kyau, ya taimaka a wajen samun
sha’awata a gidan tv, sai kuma wasu
shirye-shiryen su.

Nazari akan tashar Talabijin ta AREWA-24

Daga Iliyasu Muhd Wada

To amma ababe da
yawa suna daure mun kai, ganin yadda ake kashewa gidan Tv
kudi masu yawa tare da daukar
ma’aikata masu yawa, da gudanar da
shirye-shirye masu yawa wadanda ke
bukatar kudi da yawa kamin a hada su.
Kuma duk ace gidan tv yana yada shirye- shiryensa kyauta, kuma babu wasu
kamfanoni da ke daukar nauyin gidan tv,
ga zun zurutun kudin albashi da ake
fitarwa a duk kowane wata.

Wannan
shine dalili na farko da ya jawo hankali
na, na gudanar da wani gajeren binciki akan:

-Su waye ke daukar nauyin wannan gidan
Tv??

– Ko anan gaba gidan Tv zai koma na kudi
ne??

– Ko akwai wasu manufofi da sune
dalilin kafa wannan gidan Tv??

Ganin wasu shirye-shirye da suka ci karo
da al’adun Hausawa da Addininsu, kamar
shirin H Hip Hop, ko meye manufar ire-
iren wadannan shirye shirye??

Wannan
sune kawai dalilina na gudanar da wannan bincike da nayi, kuma na
samu bayanai da suka gamsar dani, na
wa dannan tambayoyi.

1. Mai karatu SHIN
KO KA SAN CEWA
Arewa24 gidan tv America ne, Karkashin
kulawar Federal bureau of Investigation Washington.

2. Mai karatu SHIN KO KA SAN CEWA
wannan gida Tv an ware masa
zunzurutun kudi har Dala Miliyan 60 ($
60m)

3. Mai karatu SHIN KO KA SAN CEWA An gina wannan gidan Tv domin rikicin da
yake faruwa na BOKO HARAM. A tunanin
su wannan gidan Tv zai taimaka wajen
dauke hankalin samari daga zurfafa ga
Ilimin Addinin Islama wanda suke
tunanin kan iya taimakawa wajen kirkiro kungiyoyi tare da mara masu baya iren-
iren BOKO HARAM. Ta hanyar kirkiro
shirye-shirye irinsu H Hip Hop wanda ake
tunanin zai yi korarin da kushe zafin kan
addini ga matasa, Kamar shirin zauren
malamai; wanda akoda yaushe yana Magana ne akan JAHADI, ta hanyar tara
wasu malamai da basu yi fice a wannan
yanki namu ba akan karantarwar addini.
Amma suke kokarin bayar da ma’anar
JAHADI a muslunci da kashe-kashen sa.

4. Mai karatu SHIN KO KA SAN CEWA shirin DADIN KOWA babbar manufar shirin ita
ce; daga karshe a nuna yadda malaman
Addini ke komawa ‘yan boko haram, tare
da amfani da matasa.

5. Mai karatu SHIN KO KA SAN CEWA yana
daya daga cikin manufar kafa wannan gidan Tv, daidaita matsayin Maza da Mata
acikin al’ummar Arewa, ta hanyar amfani
da shirye-shirye iri daban daban

6. Mai
karatu SHIN KO KA SAN CEWA
dukkanin shirye-shiryen wannan gidan Tv
ana tace su ne kadai anan Nigeria (Shooting and Editing) Amma sai ankai su
America ake sakasu a satellite (Airing)

7. Mai karatu SHIN KO KA SAN CEWA wasu
manufofin kafa wannan gidan Tv, ko
ma’aikatan wannan gidan bazasu san su
ba a yanzu (Kasan cewar muna fama da rashin aikin yi sosai a wannan kasa, shi ke
sa ba wani cikakken bin cike da mutanen
zasu yi a yanzu, su dai bukatarsu su samu
a ikin yi) Domin turawa sun yi nisa wajen
boye manufarsu, sai tafiya tayi nisa sosai
zasu rika fitowa a fili.

8. Mai karatu SHIN KO KA SAN CEWA Duk
shirye-shiryen da kake gani a yanzu an
a shirya su ne domin jawo hankalin jama’a
ga wannan gidan Tv, amma cikakkiyar
manufar sai nan gaba sosai zata yi tasiri!!

Mai karatu ba ina kokarin goyon bayan kafa kungiyoyi irinsu boko haram bane,
sai dai ina tsoron, a tafi “gyaran gira a
tsone idanuwa” Sakamakon lalacewar
tarbiyar da wasu daga cikin shirye-
shiryen su zai iya haifarwa, musammam H
Hip Hop, wanda tun a yanzu ya fara daukar hankalin matasa da ‘ya’yanmu
matuka.

 Mai karatu ina tsoron ire-iren
wadannan
gidajen Tv da America ke kafawa domin
bincike na, na gano wasu da aka gina a
wasu kasashen Africa dana labarawa wanda America tayi, na kuma samu
bayanai na tasirinsu a wadannan
kasashe, wajen kokarin sauya masu
al’adu. Mai Karatu manufar wannan
rubutu nawa
shine, muyi taka tsan-tsan da wannan gidan Tv. Mu san ire-iren shirye-shiryen da
zamu bar ‘yan’yanmu suna kallo a
wannan gidan Tv.

 Daga karshe mai
karatu, ni da nake
wannan rubutu dalibi ne a Jami’a bana da
wata manufa ta kushe wannan gidan Tv, domin kona kushe shi bani da wani da
zan gabatar maka a madadinsa, face nayi
ne kawai domin fadakar da ‘yan uwa
musulmi. Idan kuma akwai akasin haka
to Allah na gani kuma zai saka masu.

Amma dai kai kanka mai karatu kayi naka binciken, domin na tabbatar da
cewa wannan rubutu nawa ba zai jima
akan internet ba, zasu goge shi Domin
Karin bayani mai karatu ya ziyarci
wadannan pages din;

Idan kana/kina Tantam akai to ga babbar hujja nan Ku latsa kowanne Link domin karanta Cikakken bayani da kuma dalili Na kafa wannan Gidan TV Na Arewa24.

http://www.ibtimes.com/arewa24-us-launches-nigerian-tv-station-combat-boko-haram-1595850

http://www.premiumtimesng.com/tag/arewa24

http://newsrescue.com/nwo-landed-nigeria-us-
sponsor


Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin aiki Tukuru don jin dadin ku Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin website din akwai "Home" sai ku shiga,

mungode

Muryarhausa24.com Zata Kasance Babbar Kafar Yada Labarai aduk fadin Duniya domin Bunkasa Harshen Hausa, domin Zafafan Labarai ziyarci www.muryarhausa24.com

Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com

Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin Muryarhausa24.com aduk inda kuke a fadin Duniya farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24.com shine ta fito da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi
me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@
gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki daya Amin

Source by ©Iliyasu Muhd Wada
TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user