Sunday 2 September 2018

Karanta Dalilin da yasa Jarumi Adam A. Zango ya zama mai Auri Saki A Halin Yanzu Yazama Gwauro - Mujallar Fim

Tura Wannan Zuwa
Rahoton Mujallar Fim ta watan Yuli-Agusta ta ruwaito fitaccen jarumin Fina-finai Adam A. Zango yanzu a matsayin GWAURO yake, duk kuwa aurensa biyar a baya. 
Adam A. Zango da Matarshi

Wanda hakan ya sa aka soke shi a matsayin mai auri-saki.

Wanda hakan ya hasala shi ga mayar da martani a wani faifan bidiyo. Jaridar Arewa24news ta gano cewa Zango ya dawo jihar Kano da zama Unguwar Danladi Na Sidi.

Ga rahoton da Jaridar Rariya ta taba wallafawa na aurensa sau biyar.

Adam A. Zango Ya Yi Aure A Karo Na Biyar
A ranar Asabar din da ta gabata ne fitaccen jarumin finafinan Hausan nan Adam A. Zango ya sake yin aure, wanda shine karo na biyar da jarumin ya yi aure.

Zango, ya sake yin auren sirrin ne a garin Ngaoudere, dake kasar Kasar Kamaru, inda ya auri a wata mai suna Ummu Kulsum, wadda ake yi wa lakabi da Mama.

Kara auren da Zango ya yi, ya sa yanzu haka yana da mata biyu, inda ya saki uku daga cikin matan da ya aura a baya, wadanda suka hada da matarsa ta farko, wato mahaifiyar dansa na farko, Haidar, da kuma wata da ya auro a garin Lafiayan jihar Nassarawa da kuma wadda ya yi fim din Nas da ita, wadda ita ma ake zaton sun rabu.

Idan ba a mance a kwanakin baya jaruma Nafisa Abdullahi ta bayyanawa duniya cewa tana matukar kaunar ganin sun yi aure da jarumin, wanda hakan ya sa jama’a suka yi mamakin auren sirrin da jarumin ya yi.

Adam Zango da Matarshi

Tuni dai wasu suka soma yi wa jarumin zargin mai yawan aure saki, kasancewar duk da ba wasu shekaru ne da shi sosai ba, amma yanzu aurensa na biyar kenan. Duk da cewa ya musanta cewa shi ba dabi’arsa ba ne auri saki, kawai dai ta sa ce ta fito fili.

Kalli Sababbin Hotunan Adam Zango Dasuka Jawo Cece Kuce Ashafukan Sada Zumunta-Bude Ka gansu Kasha Mamaki

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke

Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

DOMIN SAMUN LABARAI, RAHOTANNI, LABARIN BOLLYWOOD, LABARIN FINA-FINAN HAUSA NA KANNYWOOD, LABARIN WASANNI, HAUSA NOVELS, SABABBIN WAKOKIN SIYASA, TSOFAFFIN WAKOKIN HAUSA, ZAFAFAN KALAMAN SOYAYYAR ZAMANI, TSOFAFFIN WAKOKIN SIYASA, SABABBIN WAKOKIN HAUSA, FADAKARWA ,NISHAƊANTARWA, LABARIN WASANNI, GARAƁASAR KIRA DA HAWA YANAR GIZO, ILIMANTARWA DA SAURAN SU AKAN LOKACI KU CI GABA DA KASANCEWA DA MU A www.muryarhausa24.com.ng

Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com

Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode

Source: Arewa24 news
TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user