Tuesday 15 October 2019

ALLAHU AKBAR: Karanta Yadda Za'a Tashi Al-Kiyama ta Hanyar Amfani da Hasken Rana tare da Ilimin dake Cikin Hasken Rana

Tura Wannan Zuwa
Abu Zarr, yace :

"Wata rana muna tafiya tare da manzon Allah (S.A.W) sai yace dani "Ya kai Abu Zarr ko kasan a ina rana take faduwa? sai nace "Allah da manzon sa su suka fi sani, ni kam ban sani ba, ya manzon Allah ka sanar dani, sai manzon Allah (S.A.W) "Tana zuwa ta fadi a 'karkashin Al-arshin Allah ne dake can saman sama ta Bakwai, sai tayi sujuda wa Allah, sai tace ya Allah na kammala aikin da kace nayi a yau".

Yayin Faduwar Rana


Marubuci: Abdulhadi Isah Ibrahim

Sai ta sake cewa ya Allah na fita ne? na koma ne? sai Allah yace mata "Eh" ki fita, Abu Zarri yace sai manzon Allah yace dani "akwai ranar da zata nemi fitowa ta gabas kamar yadda ta saba, sai Allah ya hana ta, sai yace ki fita ta wurin da Kika shigo (ta yamma) sai ta koma ta fita ta yamma".

Karanta Sahihul Bukhariy, Hadisi na 4,802.  za kaga Hadisin.

Daga wannan ranar kuma za'a fara shirye shiryen tashin al-ƙiyama, ba da dadewa sai ayi Busan ƙaho kowa ya fadi ya mutu.

Masu binciken kimiyya  da fasaha suka ce, idan rana zata fito a kullum, idan ka lura zaka ga tana fitowa a hankali ne, hasken ta baya bayyana kamar yadda ake kawo hasken wutar lantarki lokaci guda, hakan da rana take yi rahama ce ta Allah, domin da ace rana zata rinka fitowa kamar yadda ake kawo wutar NEPA da bayan shekaru 2 baza a samu mai gani da kwayan idon sa ba a duniya, saboda karfin hasken zai rinka cutar da idon mutane saboda yana zuwa musu a lokaci guda.

Bincike ya nuna cewa hasken  rana shine "Vitamin D" da  jikin dan Adam yake bukata, idan da ace za'a rinka kawo hasken rana  kamar yadda ake kawo wutar lantarki wannan Vitamin D din bazai samu ba, kuma ko ya samu bazai amfani jikin dan Adam ba, dan haka zaka ga yaran da jikin su bai samu Vitamin D na hasken rana ba zaka ga suna da matsalar tauyewar wasu gabobin jikin su, kamar kaga kafar yaro ya gwame, kamar ya juya bai-bai.

Hakan yafi faruwa a manyan biranen da babu hasken rana sosai, yawanci yaran su acikin gida suke basu fita, shiyasa zaka ga a kasashen da aka cigaba zaka ga kullum da safe suna kai yaran su Hasken rana su kamar shanya, zaka ga an jera su acikin rana, ko suna kuka ba'a daga su, saboda su samu wannan Vitamin D din wanda Allah ne kadai yake saukar dashi daga sama a kullum.

Haka Kuma da ace za'a rinka dauke hasken rana a lokaci guda kamar yadda ake dauke wutan lantarki da mutane da dama sai sun mutu a kullum saboda daukewar hasken ranar, saboda idan kana tafiya a mota cikin hasken rana sai kuma aka dauke hasken, za ka razana, zaka dimauce, daga nan ayi ta karo ana mutuwa.

MUKALOLI MASU ALAKA:

ME YA SA AKA HALACCI SAURO?

KARANTA CUTUTTUKA GUDA 30 DA LUWADI YAKE HAIFARWA GA MAI YINSA

AKWAI ABIN AL-AJABI GA RAYUWAR WANNAN DABBA MAI YAWAN GASKE WATO KADANGARE

Amma saboda Allah mai rahama ne, sai ya rinka kawo hasken a hankali, a hankali da safe a lokacin fitowar ta, har sai idon mutane ya saba, ya karbe ta a hankali, haka idan aka tashi dauke hasken a hankali ake daukewa, ana janye hasken ana turo duhu a hankali har idanun mutane su saba da duhun, ba tare da ya cutar dasu ba, Allahu Akbar, wannan aikin Allah kadai yake iya yi.

Nan gaba akwai karin sauran bayanan da suke da alaƙa da wannan.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode








TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user