Monday 14 October 2019

WALLAHI BAZAMU YARDA BA!! SAI SUN FITO MANA DA SAURAN KANNEN MU DA SUKA SACE MANA SHEKARU UKU BAYA

Tura Wannan Zuwa
Shekaru 3 da suka Wuce a kusan lokaci daya sai da aka saci yara guda 8 Unguwar mu ta Hotoron Arewa.

Jerin Sunayen yaran da aka sace...


Na tuno irin Halin Qunci da Damuwar da iyayen Yaran nan suka shiga. Daga cikin Yaran da aka sata a wancan lokacin akwai wani yaro da duk sanda yaga na dawo daga wajan aiki sai ya gaisheni, a dalilin haka Muka shaqu da Yaron. Lokacin da naji an Sace Yaron nan ni kaina ban iya bacci ba, ballantana iyayen Yaron.

A lokacin Iyayen Sauran yaran da aka sata daga unguwanni da suke kusa da mu da suka hadar da TINSHAMA, KAWO, BADAWA, LADANAI, HAYE, WALAWAI suka hada qungiya a tsakanin Mahaifan Yaran domin matsawa Gwamnati akan tayi bincike kan lamarin.

Amma har ya zuwa Yanzu babu amo ba labari, sai yanzu da wannan Labarin ya bayyana yanda Inyamuran nan suke safarar Yaran daga Kano zuwa can yankunan su, suna sauya musu Addini da kuma sunaye.

Bayyanar hoton daya daga cikin Yaran da aka Sata a unguwar tamu tsawon shekaru 3 da suka gabata ya qara tabbatar mana da cewa dukkanin sauran yara 47 ma suna wajan mutanen nan.

Kuma Wallahi bazamu Yarda ba... Dole Ayi Bincike...Dole sai sun fito mana da Yaran mu Dan Uwar su... Tsinannu Matsiyata, Shegu Maciya Amana..

Mu akayiwa Laifi, amma idan ka duba jaridun Kudancin Kasarnan Kaga irin zagi da rashin Mutunci da suke mana abun sai ya baka mamaki... da yawan su ma cewa suke Qarya ake yiwa yan uwansu inyamurai...

Ya zama wajibi mu bibiyi maganar satar Yara daga Kano zuwa Anambra wanda ya zama wani abin takaici dake nuna tsantsar rashin gatan talakan Arewacin Nigeria.

Domin Sama da shekaru 3, iyayen yaran ke kukan cewar Ana satar musu 'ya' ya Amma a gaskiya a Wancan lokacin basu Sami goyon baya sosai ba, sai dai Dan abin da ba'a rasa ba, a Wancan lokacin mun yi ta bin maganar tare da iyayen yaran.

Bazan ja doguwar magana ba, domin gaskiya ta fara fitowa, Amma fa akwai sauran Yara da ake nema wadanda har yanzu ba a Gano su ba.

KARANTA WANNAN: 'YAN AREWA BA MU DA HANKALI BA MU DA TUNANI

Tun Wancan lokaci iyayen yaran sun yi kungiya, suka kuma fitar da lissafin Yara 47 ne suka bace, idan Baku manta ba, har Kalanda suka fitar Mai kunshe da hotunan wasu daga cikin yaran, Dan haka ne ma yanzu za a fara fafutukar, neman ganin an fito da sauran yaran, da kuma tabbatar da adalci akan masu hannu cikin wannan balahira. Allah ya sa mu dace.

Bazamu Yadda ba! Bazamu Yadda ba!!

Justice For Kano47

Justice For Kano9

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode








TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user