Wednesday 2 October 2019

KARANTA BABBAN KALUBALEN DAKE GABAN SAMARI

Tura Wannan Zuwa
Daga cikin manyan kusa-kurai da Samari keyi a wannan lokaci shine barin zuciyarsu ta rinjaye su faɗawa soyayya da wacce basu gama sanin aihinin tarbiyyarta, addininta da nagartarta ba. Sai anyi aure ayi ta tashin-tashina zama yaƙi daɗi.


Rayuwar Samari a Wannan Zamanin


Marubuci: Imam Aliyu Indabawa

Soyayya gaskiya ce, kowa da irin kawazucin shi, amma kada ka yarda siffar mace ko iya kalamanta da wayewar ta su dulmiyaka cikin sonta, saɓanin tarbiyya da nagarta, domin kowanne namiji burinshi bai wuce samun mace tagari da zata kyautata mishi ta tarbiyyantar mishi da yara su zamo nagari ba.

Na jima ina ji ana faɗin wasu maganganu game da So cewa wai cuta ne kuma baya shawara, wannan magana ce mara makama balle tushe, a wajena wannan shaci faɗi ne kawai wanda bai taɓa faruwa dani ba kuma bazai faru ba. Kowa da irin kawazucin shi, wani karfin kawazucinshi yakan rinjaye jarumtarshi, amma ni kam jarumtata ta zarce karfin kawazucina, Wannan itace halittata kuma kaddarata.

Alaji Siffar mace, kwalliyarta, kwalisarta ko yauƙinta bai taɓa sawa naji ta burgeni, nayi mu'amala da mata iri-iri amma babu wacce tunaninta ya taɓa zuwa min akan shimfidar bacci na, tabbas ina son mace mai kyau da ado gami da aji, amma waɗan nan abubuwa sam basa tasiri cikin zuciyata, idan akwai abinda zai min tasiri bai wuce tarbiyya, addini da nagarta ba.

DUBA WADANNAN:

KARANTA ALAMOMI 10 DAZAKA FAHIMCI MACE TANA SON KA

KARANTA KAYATACCEN LABARIN WANI MUTUM DA YAYI ZINA A JAMI'A AKWAI DARASI MAI AMFANI A CIKIN LABARII

KARANTA LAIFIN ME MALAM DR ISA ALI PANTAMI YAYI WA 'YAN KWANKWASIYYA SUKE KOKARIN HALLAKA SHI?

Hajiya kada mu'amala ta hadamu dake kodai ta zahiri ko chatting ki tunanin zaki min girman kai ko rainin hankali kamar yadda kikewa sauran maza, duk kyan siffarki, bokonki da kudin babanki, ko kallo baki isheni ba wallahi, bana jura rainin wayo kuma bazan jure ba, ni ba kowa bane kuma bani da komai, amma ni mutum ne da ban yarda da wulakanci ko rainin hankali daga wajen mata ba, wannan shine sanin martabar kai.

Allah ka zaɓa mana abokan zama na nagari Amin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode








TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user