Wednesday 2 October 2019

Karanta Sakon Shugaba Buhari ga 'Yan Nigeria a Ranar Samun 'Yancin Kai na Shekaru 59

Tura Wannan Zuwa
A safiyar yau Talata 1 ga watan Oktoba 2019, wanda ya kasance Najeriya tana da shekaru 59 da “samun Yanci”Shugaba Muhammadu Buhari ya yi kira ga  yan Najeriya da su hada hannuwansu tare da marawa gwamnati baya domin samun cigaban kasar ta Najeriya a nan gaba.

Shugaba Buhari

Shugaban Buhari yayi  murnar cikar Najeriya shekaru 59 da samun ‘yancin kai,  inda yace, Najeriya za ta farfado daga cikin halin da ta jima cikinsa na tsanani nan bada jimawa ba. Sannan  yayi kira ga yan Najeriya su kara hakuri sannan  kuma suyi amfani da hanyoyin da ya  dace wajen  isarwa  gwamnati duk  korafe-korafensu da suke dashi.

Buhari ya kara da cewa, dukkan wani  hankalinmu yanzu a kan masu aikata muggan laifuka ta hanyoyin zamani wato yanar gizo, sannan  kuma masu yada labarai marasa tushe a shafukan sadarwa na zamani. Duk da cewa muna cigaba da mutunta kundin tsarin kasarmu wanda ya halarta ‘yancin fadin albarkacin baki ga ko wane dan kasa, amma kuma ba za mu zuba muna kallon wadansu tsirarun mutane na neman haddasa fitina a kasar ba.

Shugaba Buhari ya kara da cewa: Kiyayya da ganin kyashi ba komi take haifarwa ba in banda tabarbarewar kasa da kuma rashin cigaba. Ina da yakinin cewa akasarin yan Najeriya sun fi sha’awar zaman lumana da kwanciyar hankali a junasu.

A jawabin da ya gabatar ga 'ya kasar ta talabijin din Najeriya da misalin karfe 7:00 na safe, shugaban mai shekara 76, ya ce gwamnatinsa ta sha alwashin kare hakkin kowanne dan kasar.

KARANTA WANNANHanya Mafi Sauki da Zaku yi Nasara Wajen Hana Banki Cazar Muku Kudi a duk Lokacin da Zaku Fitar da Kudi

A karshe yace, kaddamar da kasafin kudin 2019 wanda aka yi a watan Yuni zai soma aiki cikin gaggawa domin ganin cewa an kammala ayyukan manya masu matukar amfani ga al’ummar  kasar ta Najeriya baki daya.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Isar da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradin Mu


Burin shafin Muryar Hausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje ɗaya a ko ina suke



Domin samun Labarai,Nishaɗi, Kalaman Soyayyar Hausawa,Bincike mai zurfi,,Tarihi,Fadakarawa,Tunatarwa, Complete Tafseer, Complete Qur'an Audio, Addu'o"in littafin Hisnul Muslimi cikin harshen Hausa, Kimiya da Fasaha,Hotuna,Hausa Comedy, Wakokin Gargajiya, Wakokin Siyasa, Wakokin Zamani, Wakokin Bege na Annabi Muhammad (SAW) , Sharhi akan al'umaran Yau da Kullum , Sharhi mai gamsarwa, tsage gaskiya dalla-dalla da dai sauran su Ku ci gaba da kasancewa da Mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda Ku Kasance a fadin Duniya.



Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.



Zaku iya aiko mana da Labari ko shawarwari, Ra'ayoyin ku ko kuma nuna gamsuwar Ku akan yadda Mu ke tafiyar da wannan Shafi mai ALBARKA aika saƙon ka/ki akan addreshin Mu Na yanar gizo muryarhausa24@gmail.com  Za muyi farin ciki da samun saƙon ka/ki

Mungode








Source: Oak TV Hausa
TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user