Monday 9 March 2020

SHIN KO YA HALATTA NA AURI KIRISTA?

Tura Wannan Zuwa
TAMBAYA

Malam musulmi zai iya auren ahlul kitab ta na addininta yana musuluncinsa?

Tambaya Mabudin Ilimi..

MarubuciDr. Jamilu Zarewa

AMSA

To Ɗan uwa Allah maɗaukaki ya halatta auren kamammu daga cikin ahlul-kitabi, wato Yahudu ko Nasara, kamar yadda ya yi bayanin hakan a cikin suratul Ma'ida a aya mai lamba ta: (5), kuma an samu wasu daga cikin sahabai, sun aure su kamar Usman ɗan Affan - halifa na uku a musulunci- ya auri Banasariya, haka Dalhatu ɗan Ubaidillah ya auri Banasariya, sannan Shi ma Huzaifa masanin sirrin Annabi ﷺ ya auri Bayahudiya, Allah ya kara musu yarda.

Duba: Ahkamu-ahlizzimah 2\794.

Saidai malaman wannan zamanin suna cewa, abin da ya fi shi ne rashin auren Ahlul-kitab a halin yanzu, saboda yadda zamani ya canza, domin da yawa idan mijinsu musulmi ya mutu yaran suna zama cirister, kai wani lokacin ko da sakinta ya yi za ta iya guduwa da yaran, sannan zai yi wuya ka samu kamammu waɗanda ba su taɓa zina ba a cikinsu.

Wasu kasashen kuma idan za ka auri Kirista daga cikinsu dole sai ka yarda da dokokin ƙasarsu, a lokuta da yawa kuma za ka samu dokokin sun saɓawa ka'idojin musulunci.

Allah ne mafi sani.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com.ng munayin
aiki tuƙuru don Ilimantarwa da Faɗakarwa.

Ku ci gaba da kasancewa da mu a www.muryarhausa24.com.ng   a duk inda ku kasance a faɗin Duniya.

MURYAR HAUSA24 FARIN CIKIN AL'UMMA.

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: