Tuesday 23 April 2024

Karanta Labarin Gaggawa Da Hakuri Da Lokaci

Tura Wannan Zuwa

Watarana, wasu matasa biyu Gaggawa da Hakuri suna tafe a cikin wani ƙungurmin daji mai suna Duniya, a ƙoƙarin su na neman wani lambu mai suna Nasara. Tare da su akwai wani yaro ɗan ƙarami, mai suna Lokaci, wanda yake yi musu rakiya.


LABARIN GAGGAWA DA HAKURI DA LOKACI
Hoto: PNGTREE


 

Marubuci: Muhammad Musa Yelwa


Su na tafe suka isa wani kwazazzabo mai yawan duwatsu, wanda kuma a wurin ne ɗan rakiyar tasu Lokaci ya yi tuntuɓe da dutse, ya faɗi! Kodayake, ya lallaɓa ya yi ƙarfin hali ya tashi, sai dai yanzu tafiyar tasa babu sauri, sakamakon jan-ƙafa da yake yi.


Su na cikin wannan hali ne kuma Gaggawa ya hango wancan lambu da suke ta faman nema. Don haka, nan take ya ruga a guje, ya nufi wurin.


Lokaci ya ƙwalla masa kira:

“Haba Gaggawa, ya za ka yi mana haka? Ka jira mu mu shiga tare mana.”


Gaggawa ya ci gaba da gudunsa, ba tare da ya ko waiwaya ba. Ganin haka, Haƙuri ma ya ƙara ɗaga murya, yana cewa: “Kai kuwa wanne irin ci-da-zuci kake haka? Ka tsaya mu mana.”.


Gaggawa ya juyo a fusace ya ce da shi: “Kai rufe min baki, ni ba ni da kai.”.


Lokaci ya juya ya dubi Haƙuri ya ce: “Ka ji fa, wai ba shi da kai. Yana nufin ya haukace ne?”.


Haƙuri ya ce: “A’a, yana nufin dai ba shi da kai ne, wataƙil.”


Lokaci ya gyaɗa kai, sannan ya ce: “To kai me ya hana ka ka bi shi?”


Haƙuri ya ce: “Ni ba na tashi ai.”


Lokaci ya ce: “Kana nufin ba ka da fuffuke kenan?’’


Ya ce: “Ina nufin ba na gaggawa.”


Lokaci ya ce: “To me ya sa?”


Ya ce: “Saboda ina sane da cewa, ko da na je zan taar da ƙofar lambun a rufe. Tun da dai babu wani abu da yake faruwa ba tare da lokaci ba. kuma ga ka a nan.” 


Lokaci ya yi murmushi, sannan ya ce: “Hakika ka yi kyan kai. Tabbas mabuɗin yana tare da ni, amma tun da ka yi haƙuri, karɓi mukullin daga yau na ba ka kyauta, ya zama naka.” 


Suna ƙarasawa bakin lambun kuwa, Haƙuri ya sa mabuɗi ya buɗe lambun Nasara, ya yi bankwana da lokaci ya shiga. Yana tunanin shin ko a ina Gaggawa ya maƙale!?”


Yayin da Lokaci ya juya don ci gaba da tafiya, sai ya hangi Gaggawa kwance magashiyyan a bayansa, yana numfarfashi, ashe zuwa ya yi ya riƙa bangazar ƙofar ba ta buɗe ba har sai da jikinsa ya yi la’asar (Sanyi). Can cikin wata murya mai raurawa, ya ce wa Lokaci: “Don Allah ko akwai wani mabuɗin ka taimaka ka ba ni, ni ma na shiga?”


Lokaci kuwa ya ce da shi: “Ai mabuɗin Nasara ɗaya ne, kuma tuni yana tare da Haƙuri. Da ka yi haƙurin jira na, da ka samu, amma da yake ba ka yi ba, ga shi nan har na riga na wuce. Kuma ni idan na wuce ba na dawowa baya.” .


Don ci gaba da samun ire-iren waɗannan, ku ci gaba da kasancewa tare da mu a kodayaushe.

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user