Monday 25 December 2017

Karanta Kaji Dalili: Ko 2019 na sake fitowa Takara Ni ne zan lashe Zaben-Muhammadu Buhari

Tura Wannan Zuwa

Shugaban Nigeria Muhammadu Buhari ya ce goyon bayan da 'yan Nigeria ke nuna masa ita ce babbar garkuwarsa.

Ya bayyana haka ne a wani shirin talbijin da fadar shugaban kasar ta dauki nauyi da aka watsa ranar Lahadi.

Shugaba Buhari ya ce a duk lokacin da ya yi Sallah ya kan gode wa Allah da ya sa talakawa ke matukar kaunarsa kuma suka yarda da shi.

Shirin dai ya tattauna ne da shugaban kasar tare da jin ra'ayoyin wasu fitattun 'yan Najeriya.

Daga cikin su har da tsohon shugaban kasa Ibrahim Babangida da wasu ministocin gwamnatin wadanda suka yi tsokaci kan halayyar shugaban kasar da kuma salon mulkinsa.

BBC Hausa ce ta wallafa Labarin Cewa" Talakawa na matukar kaunata - Buhari".

Martani

Wasu masu sharhi a shafukan sada zumunta da muhawara sun yi ta sukar shirin da aka watsa ta gidan talbijin.

Wani dan Jarida mai suna Ja'afar Ja'afar ya rubuta a shafinsa na Facebook cewa;

".....na kwashe sa'a guda ina bata lokaci wajen kallon shirin da babu komai a ciki illa shirme ..Ban yahewa wallah!

Shi kuwa Idris Mohammed ya rubuta a shafinsa na Facebook cewa;

''Kasancewar mutane miliyan 12 ne suka zabi shugaba Buhari har yanzu suna goyon bayansa fiye da shekaru goma, babu wani dan siyasa da ya kama kafa sa.. Ko yau aka yi zabe shine zab na."

Sai dai wani mai suna Yakubu Lere cewa ya yi;

''Na fara kallon shirin a matsayina na kwararren ma'aikacin watsa labarai fiye da shekaru 30, amma na ji takaici har sai da na kashe akwatin talbijin d na".....

Wasu dai sun zargi fadar shugaban kasar da neman karkata hankalin 'yan Nigeria game da matsalar karancin mai da ake fuskanta a halin yanzu.

Sai dai mai ba shugaba Buhari shawara kan harkokin watsa labarai Femi Adesina ya mayar da martani ga masu sukar gabatar da shirin a daidai wannan lokaci.

Mr Adesina ya wallafa a shafin sa na Facebook cewa duk da wahalar karancin mai da ake fuskanta na kankanen lokaci, ya zama wajibi a waiwayi wani batu mai farantawa al'umma rai.

Wasu masu lura da al'amura a Najeriyar dai na ganin wannan shiri tamkar sharar fage ne kan shirye shiryen shugaba Buhari na sake tsaya wa takarar 2019.

Sai dai kawo yanzu shugaba Buhari bai fito fili ya bayyana aniyarsa ta sake tsayawa takarar ba.

Shafin komai da ruwanka, Dadinkowa24 munayin aiki Tukuru don jin dadin ku

Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa kamar haka dadinkowa24.blogspot.com

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin  website din akwai "Home" sai ku shiga, mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa nayau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin Cikin Mu Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com

Idan kana/kina da Labarin daku keson asanarwa da Duniya, ko Tambaya,Shawarwari,Hausa Novels, Nishadantarwa,Ilimantarwa,Ko Neman Sani akan ranakun dazamu cigaba dakawo muku Posting na Hausa Novels da Sauran su, zaku iya tuntubar ma'aikatan mu kuturo da Sunan Ku tareda Addreshin Ku tawannan Email din Officialdadinkowa24@gmail.com kyautane zamuyi muku komai don cigaban Al'ummar Hausa bama bukatar kudinka sai dai idan kaikayi niyyar Turowa don siyan Data Saboda acigaba dayin Posting a Kodayaushe batareda dakatawa ba, Website din Mu bashi da Alaka ta kusa ko tanesa da Wani/Wata Dan Siyasa/'Yar Siyasa afadin Duniya Burin mu shine musamu amincewar Al'umma aika da Gudunmawarka,Labari,Shawara da sauran su a Addreshin mu na email ✉💌📩 officialdadinkowa24@gmail.com

Always Visit==http://dadinkowa24.blogspot.com

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga Suleman Abubakar saboda awajensa musami Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani ba, adinga yimana Uziri

ALLAH yabar Zumunci Amin

Source By ©Bbc Hausa

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: