Wednesday 3 January 2018

Kalli Abubuwa uku da Shekau ya fada a sabon bidiyonsa

Tura Wannan Zuwa Ga

Shugaban Boko Haram, Abubakar Shekau, ya fito a wani faifan bidiyo inda ya ce kungiyarsa ce ta kai hare-hare a arewa maso gabashin Najeriya.

Bidiyon mai tsawon minti 31 da dakika 53 ya nuna shugaban Boko Haram din sanye da farar riga tare da bindiga a jingine a kafadarsa.

Shekau dai ya yi magana ne cikin harshen Larabci da Hausa kuma ya karanta da yawa daga cikin maganar da ya yi da harshen Larabci ne daga cikin wata takarda rike a hannunsa.

Da yake karatu daga cikin takardar ya yi ta runtsa ido, abin da ke nuna cewa ba ya ganin abin da yake karantawa sosai.

Ba za a iya tabbatar da lokacin da aka dauki sabon bidiyon na Boko Haram ba.

Mu muka kai hare-hare .

Shugaban Boko Haram ya ce mayakansa ne suka kai hare-hare a Maiduguri da Damboa da Gamboru.
Sannan ya ce suna nan lafiya ba abinda ya same su.

Bidiyon ya nuna harin da Boko Haram ta kai wani shingen binciken sojoji a kauyen Molai da ke kusa da Maiduguri a ranar kirsimeti, harin da sojoji suka ce sun murkushe mayakan kungiyar bayan shafe lokaci mai tsawo suna musayar wuta.

An nuna 'yan Boko haram rike da manyan bindigogi, wasu cikin budaddiyar mota wasu saman babur suna harbi amma ba tare nuna wadanda suke musayar wutar da su ba.

Bidiyon ya nuna yadda mayakan suka kwashi makamai da motocin sojoji da na gwamnatin Borno.

Martani ga Janar Rogers

A cikin bayaninsa, Shekau ya ambaci sabon shugaban rundunar Operation lafiya Dole da ke yaki da Boko Haram, Manjo-Janar Nichola Rogers, wanda ya yi kira ga 'yan Boko Haram su tuba.

Shugaban na Boko Haram ya mayar da martani inda ya ce kwamandan sojin Najeriyar ne ya kamata ya tuba.

Sannan ya ce ba abin da Sojoji da 'Yan sanda za su iya yi akan su.
Birnin Kudus
Shekau ya tabo batun Birnin Kudus, wanda shugaban Amurka Donald Trump ya amince a matsayin babban birnin Isra'ila.

A cikin bayaninsa, ya ce Falasdinawa da ke ikirarin 'yan kishi ne da gangan suke yi.
"Ba da gaske suke ba, inda da gaske suke da ba za su bari wani ya karbi masallaci ya je yana abin ya ga dama ba" a cewar shugaban na Boko Haram.

Sannan ya soki Saudiya a matsayin kasar da ke shawara da Yahudawa.
Boko Haram har yanzu dai barazana ce.

An shafe watanni Shekau bai fitar da bidiyo ba, lamarin da wasu ke dangantawa da cewa alamu ne na karya lagon kungiyar Boko Haram.

Bidiyon na zuwa ne kwana daya bayan shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, a sakonsa na sabuwar shekara ya ce dakarun kasar sun samu galaba a kan 'yan Boko Haram.

Sai dai har yanzu Boko Haram na ci gaba da zama barazana ga tsaron Najeriya da kasashen da ke makwabta da ita.

Tun da farko dai rundunar sojin Najeriya ta ce ta dakile harin da Boko Haram ta kai a Molai a ranar Kirsimeti.

Kwamandan rundunar Lafiya Dole Janar Nicholas Rogers ya ce dakarun sojin sun yi bata-kashi da mayakan Boko Haram bayan da suka farma wani wurin binciken sojoji da ke wajen birnin Maiduguri.

Shafin komai da ruwanka, Dadinkowa24 munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address
kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa
kamar haka dadinkowa24.blogspot.com

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin
Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://
dadinkowa24.blogspot.com

Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Dadinkowa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Babban Shafi a Yanar Gizo da
ke gabatar da
shirye-shiryensa a cikin harshen Hausa Zalla
cikin 24 Hours ba tareda kakkautawa ba

Burin shafin DADINKOWA24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

ALLAH yabar Zumunci Amin

Source By ©Bbc Hausa

TURA WANNAN ZUWA GA

Mawallafi: verified_user

0 comments: