Tuesday 9 January 2018

Labari: Malaman makarantun Kaduna sun bijirewa El-Rufai

Tura Wannan Zuwa

Malaman Makarantun firamare da sakandare sun soma yajin aikin sai baba ta gani a jihar Kaduna arewacin Najeriya.

Kungiyar Malamai ta kasa NUT ce ke jagorantar yajin aikin da aka soma a yau Litinin domin adawa da matakin gwamnatin jihar na korar Malaman Firamare 22,000.

Wakilin BBC Nura Muhammed Ringim ya ce makarantu sun kasance a rufe, bayan da malamai suka kauracewa aji a yau Litinin da daliban ya kamata ace sun koma makaranta bayan hutun kirsimeti da sabuwar shekara.

Ya ce kungiyar Malaman ta bi makarantu a sassan jihar tana kafe sanarwar shiga yajin aikin.

Tun da farko kungiyar Malaman ta ba gwamnati wa'adin mako biyu kan ta janye matakin korar malaman kafin shiga yajin aikin, wanda ya shafi makarantun Firamare da Sakandare.

Gwamnatin Jihar Kaduna ta jarraba malaman firamare guda 33,000, amma 66 bisa 100 ne gwamnatin ta ce suka fadi jarabawar.

A watan Disemban da ya gabata kotun ma'aikata ta kasa ta ba gwamnan jihar Nasir El- Rufa'I umurnin dakatar da matakin korar malaman.

Amma tuni gwamnatin ta aike da takardar sallama ga malaman da suka fadi jarrabawar da aka shirya mu su ta matakin 'yan aji hudu don jarraba kwazonsu.

Kuma a cikin sanarwar da gwamnatin Kaduna ta fitar game da yajin aikin, ta ce ba gudu babu gudu ba ja da baya kan aniyar korar malaman tare da barazanar daukar mataki mai tsauri kan duk malamin da ya ki fitowa kan aikinsa.

Shafin komai da ruwanka, Dadinkowa24 munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address
kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa
kamar haka dadinkowa24.blogspot.com

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin
Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://
dadinkowa24.blogspot.com

Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Dadinkowa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Babban Shafi a Yanar Gizo da
ke gabatar da
shirye-shiryensa a cikin harshen Hausa Zalla
cikin 24 Hours ba tareda kakkautawa ba

Burin shafin DADINKOWA24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

ALLAH yabar Zumunci Amin

Source By ©Bbc Hausa

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: