Thursday 11 January 2018

Yarinya me Lokaci: Hukumar tace fina-finai ta yafe wa Rahama Sadau-Karanta Kaji Dalilin Yafewa Rahama Sadau

Tura Wannan Zuwa

Hukumar tace fina-finai ta jihar Kano ta ce ta yafe wa fitacciyar jarumar fim Rahama Sadau dukkan laifukan da ta yi, wadanda suka janyo aka hana ta yin fim.

Shugaban hukumar, Isma'ila Na'abba Afakalla, ya shaida wa Nasidi Adamu Yahaya cewa, "A shirye muke mu soma tace fina-finan da za ta rika fitowa a ciki da kuma wadanda take daukar nauyinsu".

Afakalla ya kara da cewa sun dauki wannan mataki ne bisa la'akari da gafarar da jarumar ta nemi a yi mata kwanakin baya.

A cewarsa, "Wannan baiwar Allah ta zo ofishina a shekarar da ta wuce inda ta nemi gafara kan abubuwan da ta yi a baya; na gaya mata ta je ta nemi gafarar Gwamna da Sarkin Kano kuma ta fito a gidan rediyo ta nemi afuwarsu da ta al'umar da take ciki.

"Don haka a matsayinmu na 'yan-Adam wadanda kullum muke cikin kuskure, so muke a ja mutum a jiki kada ya fandare, shi ya sa muka yafe mata. Duk lokacin da mutum ya yi laifi ba a rufe masa hanyar tuba. Kuma ko yanzu ta kawo fim za mu tace shi", in ji shi.

A watan Oktoban da ya gabata ne shahararriyar jarumar ta fito fili ta nemi gafarar duk wani mutum da bai ji dadi ba sakamakon fitowar da ta yi a wani bidiyon waka tana "rungumar" wani mawaki.

A wata wasikar da ta aike wa kungiyar masu shirya fina-finai ta kasa, MOPPAN, Rahama ta nemi afuwa a kan abin da ta yi, tana mai cewa "kuskure ne," kuma za ta "kiyaye gaba".

A wancan lokacin, Shugaban MOPPAN Kabiru Maikaba ya shaida wa BBC cewa kungiyar za ta sanar da matsayin da ta dauka a kan afuwar da jarumar ta nema bayan shugabanninta sun tattauna a hukumance.

Sai dai har yanzu kungiyar ba ta sanar da matakin da dauka ba.
Wata majiya ta shaida wa BBC cewa kan 'yan kungiyar ya rabu game da batun - inda wasu ke son a yafe mata yayin da wasu suka ki amincewa da hakan.

Da alama wannan ne ya sa fitaccen darakta Yaseen Auwal wanda ke goyon bayan jarumar ya nuna matukar bacin ransa game da kafar-ungulun da yake ganin wasu na yi ga batun.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Instagram, daraktan ya yaba wa shugaban hukumar tace fina-finan jihar Kano saboda kokarin da yake yi wurin ganin an dawo da ita fagen fim, sannan ya soki mutanen da ke kawo tsaiko cikin lamarin.

A cewarsa, "Allah Sarki bawan Allah Ismai'ila Na'abba, muna kara godiya bisa abin da ka yi a kan Rahama Sadau. Allah ya saka da alheri...ka yi naka mun gode; ka bar mu da ragowar...".

Rahama Sadau, wacce yanzu haka take kasar Cyprus inda take karatu, na shirin fitar da sabon fim dinta mai suna Dan Iya a wannan shekarar.

Shafin komai da ruwanka, Dadinkowa24 munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku

Mun kudiri aniyar tsage gaskiya
na bada labarai da suka hada da
harkokin yau da kullum Da zummar
samar da zaman lafiya da kuma
daukaka kima da martabar
al’adun Hausa.

Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Kada Ku manta in zaku ziyarci website din mu
akan wayar/kwamfiyutar Ku zakusa address
kamar haka
dadinkowa24.blogspot.com banda sa www
kuma batareda bayarda sarari wajen sa
address din ba sannan da kananun Haruffa
kamar haka dadinkowa24.blogspot.com

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Dadin
Kowa24 don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://
dadinkowa24.blogspot.com

Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Dadinkowa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Babban Shafi a Yanar Gizo da
ke gabatar da
shirye-shiryensa a cikin harshen Hausa Zalla
cikin 24 Hours ba tareda kakkautawa ba

Burin shafin DADINKOWA24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

ALLAH yabar Zumunci Amin

Source By ©Bbc Hausa

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: