Thursday 29 March 2018

Karanta Kaji: Shin ko Shugaba Buhari ya Cancanta a Bashi Lambar Yabo akan Yadda yake Mulki???

Tura Wannan Zuwa

Cibiyar The King Center, wacce ke adana tarihin fitaccen bakar fatar nan na Amurka, marigayi Martin Luther, ta nesanta kanta daga lambar yabon da aka bai wa Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya.

Ranar 26 ga watan Maris ne wasu da aka ce iyalin Martin Luther ne suka ziyarci fadar shugaban Najeriya tare da rakiyar mai ba shi shawara kan harkokin 'yan kasar mazauna kasashen waje, Abike Dabiri, inda suka ba shi lambar yabon da ake kira 1st Black History Month National Black Excellence and Exceptional African Leadership Award 2018.

Sun ce an ba shi lambar yabon ne saboda jajircewarsa wurin mulki na gari.
Sai dai a wani sako da cibiyar ta wallafa a shafinta na Twitter ranar 28 ga watan Maris ta ce "ba cibiyar The King Center ce ta bai wa Shugaba Buhari lambar yabo ba, kuma ba 'ya'yan MLK da Coretta Scott king ne suka ba shi ba."

Kun san mutanen da 'suka yi wa Buhari magudin zabe a 2007'?
Obasanjo ya ga baiken Buhari kan kasuwancin Afirka
'Yan sanda sun kama Sarki Sunusi 'na bogi'
Fadar shugaban kasa ta shaida wa BBC cewa lambar yabon ba ta boge ba ce kamar yadda wasu ke zata.

A cewarta, nan gaba kadan za ta fitar da sanarwa domin yin karin haske kan batun.

Wannan batu dai ya jawo zazzafar muhawara a shafukan sada zumunta, inda wasu ke caccakar shugaban kasar "saboda bai wa kasar kunya a irin karairayin da take yi da zummar boye gazawarta wurin gudanar da mulki".

Wani mai amfani da shafin Twitter Donn Rolly ya rubuta cewa: "Amma mutane mu duba mana. Yaya za a damfari Shugaba Buhari irin haka da lambar yabon boge kamar wacce aka yi a Aba."

Sai dai yayin da 'yan kasar da dama ke kushe tare da ganin baiken gwmnatin Buharin kan wannan lambar yabo, wasu kuwa suna ganin lambar yabon ba ta boge ba ce, inda har suke nuna goyon bayan gwamnatin.

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku
Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Muryarhausa24.com don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum

An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com
Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Muryarhausa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki
daya Amin Summa Amin.

Source by ©Bbc Hausa

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: