Sunday 29 April 2018

Karanta Kaji: Abubuwa 4 da ya kamata ku sani dangane da ziyarar Buhari Kasar America

Tura Wannan Zuwa

Shugaba Buhari ne shugaban kasar Afrika na farko da
gwamnatin Trump ta gayyata zuwa fadar gwamnatin ta domin
tattaunawa.

1. Yaki da ta'addanci: Najeriya ta shiga shekara ta tara tana
yaki kungiyar Boko Haram a yankin arewa maso gabas ga
kuma sabon rikicin makiyaya da ya kunno kai.
Shugabannin biyu zasu tattauna hanyoyin da zasu hada karfi da
karfe domin kawo karshen aiyukan ta'addanci a Najeriya.

Trump ya taba sukar tsohon shugaban kasar Amurka Barack
Obama saboda kin sayar wa da Najeriya makamai.

2. Inganta dangantaka tsakanin kasar Amurka da Najeriya da
kasashen Afrika: Gayyatar shugaba Buhari wata manuniya ce
cewar kasar Amurka ta yarda da cewar Najeriya ce ga
kasashen Afrika.

Kalaman kaskanci da shugaba Trump ya yi a kan kasashen
Afrika a watannin baya ya jayo barkewar cece-kuce da
kunakuni daga shugabannin duniya da 'yan Afrika.

3. Tazarce: Shugaba Buhari da Trump zasu sake yin takara
domin zarcewa a kan mulki. Shugaba Buhari zai yi amfani da
damar ziyarar domin bayyana irin nasarorin da gwamnatin sa ta
samu a bangaren noma domin samun goyon bayan kasar
Amurka a zaben shekarar 2019.

4. Tattalin arziki: Kasar Amurka ta nuna damuwar ta a
kwanakin baya dangane da yadda kasar China ke yunkurin
mamaye kasuwancin kasashen nahiyar.

A kwanakin baya kasar Amurka ta turo tsohon sakataren
gwamnatin ta, Rex Tillerson, domin nunawa kasashen Afrika
illar kulla harkokin tattalin arziki a nahiyar Afrika. Saidai bai
karasa ziyarar ba shugaba Trump ya kore shi daga aiki.

Source by ©Hausa Naija

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: