Monday 9 April 2018

KARANTA KAJI: Nayi Amannar Cewa Yan Nigeria bazasu Bani Kunya ba Wajen Sake Zabena a 2019- Muhammadu Buhari

Tura Wannan Zuwa

Shugaban Najeriya Muhamamdu Buhari ya sanar da cewa zai sake tsayawa takarar shugabancin kasar a shekarar 2019.

Mai taimakawa shugaban na musamman kan shafukan sada zumunta Bashir Ahmad ne ya sanar da hakan a shafinsa na Twitter a ranar Litinin.

Wannan sanarwa dai ta zo ne bayan da aka shafe swatanni ana yada jita-jitar ko zai tsaya ko ba zai tsaya ba takarar ba.

Sai dai tun kafin shugaban ya bayyana aniyar tasa akwai wadanda suke ganin bai kamata ya nemi tazarce ba, ciki har da tsohon Shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo.

'Buhari ba zai so ya bar gwamnati yanzu ba'
Jama'a da dama na ci gaba da bayyana ra'ayoyinsu kan sanarwar da Shugaba Buhari ya yi cewa zai nemi tazarce a zabe mai zuwa.

Sai dai Dr Suleiman Amu Suleiman, masanin siyasa a Jami'ar East Anglia da ke Birtaniya, ya shaida wa BBC cewa bai yi mamakin sanarwar ba.

Ya ce hauhawar da farashin mai da ake yi a baya-bayan nan, ya nuna cewa kudi zai ci gaba da shigowa gwamnati domin samun damar yin ayyuka da cika alkawuran da ya dauka sakamakon lokacin da ya samu gwamnatin cikin talauci.
Don haka babu wanda zai so ya bar gwamnati a yanzu.

Abu na biyu shi ne, shugaban ya samu lafiya sosai fiye da shekarar da ta gabata, lokacin da hankalin wasu da dama ya tashi saboda tabarbarewar lafiyarsa.

A yanzu ya samu kwarin gwiwa yana tafiye-tafiye ba tare da wata matsala ba..

Abu na uku shi ne, ' Ina ganin shi kansa Shugaba Buhari yana ji a zuciyarsa cewa bai taka rawar azo-agani ba, a don haka yana so a sake bashi dama domin ya gyara'.
Nasarar da ya samu ba ta kai wacce ya samu ba a lokacin da ya shugabanci Hukumar Kula da Kudaden da ake samu na rarar man fetur inji Dr Suleiman.

Idan har ya wuce to zai samu damar yin ayyuka ba tare da wani dabaibayi na siyasa ba irin wanda ya makale shi a shekara hudunsa na farko.

Sai dai ' Ba zan iya cewa zai kai labari ba tukunna domin wannan zai dogara ne kan irin shirin da 'yan adawa suka yi, da yadda ra'ayin 'yan Najeriya zai karkata kafin lokacin'.
Dama dai tun kafin wannan sanarwa wasu masu sharhi su ka fara tofa albarkacin bakinsu kan yiwuwar sake tsayawar Buharin takara.

Malam Jafar Jafar wani mai sharhi ne kan harkokin siyasar Najeriya, kuma ya ce yana ganin duk wani dan siyasa da yake neman takara a jam'iyyar APC yana bata wa kansa lokaci ne kawai, "matukar Shugaba Buhari zai sake yin takara."

Ya ce: "Idan har Buhari zai yi takara, to babu makawa jam'iyyarsa shi za ta tsayar a zaben 2019."
"Kuma da wahala a ce ba zai yi takara ba," in ji shi.

Malam Jafar ya ce zabin da ya rage masu muradin yin takara a jam'iyyar APC shi ne kawai su sauya jam'iyya.
"Ga jam'iyyu nan da yawa. Idan dai ba a yi murdiya ba a zaben 2019, akwai yiwuwar jam'iyyar APC za ta iya faduwa zabe."

"Saboda a gaskiya farin jinin jam'iyyar da na Shugaba Buhari ya ragu sosai."

Zuwa yanzu dai Shugaba Buharin da kuma gwamnan jihar Ekiti da ke kudu maso yammacin kasar Ayo Fayose ne kawai suka bayyana aniyarsu ta tsayawa takarar shugabancin kasar.

Shugaba Buhari ya ci zabe ne a shekarar 2015

Ya yi takara sau hudu a jere kafin ya samu nasara

Shi ne dan takara daga jam'iyyar adawa na farko da ya doke shugaba mai ci a tarihin Najeriya

Ya samu kuri'u 15,424,921

Ya yi ta fama da jinya a shekarar 2016 inda ya shafe fiye da wata uku a Birtaniya

Bayani kan Shugaba Muhammadu Buhari a takaice:

Shekararsa 72

An zabe shi a matsayin shugaban kasa a zaben 28 ga Maris 2015

Ya yi shugaban mulkin sojan Najeriya daga 1984 zuwa 1985

An hambare shi a juyin mulki

Ya samu shaidar rashin kare hakkin dan adam

An yi amanna ba shi da cin hanci da rashawa

Mai ladabtarwa ne - a kan sa ma'aikatan gwamnati tsallen kwado idan suka yi lattin zuwa aiki

Musulmi ne daga arewacin Najeriya
Ya tsallake rijiya da baya a wani hari da Boko Haram ta kai masa

Shafin komai da ruwanka, Muryarhausa24.com munayin
aiki Tukuru don jin dadin ku
Isar
da bayanai akan lokaci ba tareda son
zuciya ba shine muradinmu

Ku hanzarta sanar da 'Yan Uwa da abokanan
Arziki sunan Website din Mu me Albarka, don
ganin sabbin posting din Mu sai ku duba cikin
website din akwai "Home" sai ku shiga,
mungode

Ku cigaba da Kasancewa da Website din Muryarhausa24.com don samun abubuwan more rayuwa na
yau da Kullum

An kirkiri Wannan Shafi domin
bunkasa Harshen Hausa ako ina afadin Duniya
Labari iri daban-daban, farin cikin Ku shine Farin
Cikin Mu Always Visit==http://www.muryarhausa24.com
Ku Cigaba da Kasancewa da Shafin
Muryarhausa24 aduk inda kuke a fadin Duniya
farin cikin ku shine Farin cikin Mu

Munayin iyakar bakin kokarin mu don baiwa me
hakkin rubutu hakkinsa, ma'ana idan mun samu
Rubutu daga Suleman Abubakar to zamusa daga
Suleman Abubakar saboda awajensa musami
Rubutun koda bashi yayi ba to mu bamu Sani
ba, adinga yimana Uziri

Burin shafin Muryarhausa24 shine ta fito
da kyawawan manufofi, tsari, Nagartar masu jin
yaren Hausa a dukkan fadin Nigeria da kasashen
da suke makwabtaka da ita kuma ta hada kan
masu jin yaren Hausa waje daya a ko ina suke

KARIN BAYANI

Zaku iya aiko mana da labari,Nishadi,Fadakarwa,Hausa Novel,Ra'ayi,Labarin Soyayya, Sharhi ko nuna gamsuwar Ku akan yadda muke tafiyar da wannan shafi me Albarka aika sakon ka anan muryarhausa24@gmail.com mungode

Allah ka daukaka harshe Hausa dama Kasa baki
daya Amin Summa Amin.

Source by ©Bbc Hausa

TURA WANNAN ZUWA

Mawallafi: verified_user

0 comments: